Home DUNIYA Majalisar Dinkin Duniya Tayi Tir da Mamayar Rasha Kan Ukraine

Majalisar Dinkin Duniya Tayi Tir da Mamayar Rasha Kan Ukraine

Majalisar Dinkin Duniya ta kada kuri’ar yin tir da Rasha kan mamaye wasu sassan Ukraine da ta yi, matakin da shugaban Amurka Joe Biden ya ce sako ne mai karfi ga takwaransa Vladmir Putin.

Kasashe 143 ne suka goyi bayan kudurin na yin tir da Rasha a zauren Majalisar Dinkin Duniyar, inda 5 suka hau kujerar naki, sauran kasashe 35 kuma suka kauracewa zaman, wadanda suka hada da China, India, Afirka ta Kudu da kuma Pakistan, duk da matsin lambar da Amurka ta rika musu kan su yi tir da Rashan; kamar yadda jaridar Reuters ta ruwaito.

Kudurin dai ya yi tir da matakin Rasha, na shirya  zaben raba gardama a cikin iyakokin Ukraine” da kuma “yunkurin mamaye yankuna hudu na kasar ta karfin tsiya da shugaba Vladimir Putin ya sanar a watan jiya.

Ko a watan Satumban da ya gabata, sai da Majalisar ta nufaci kada makamanciyar kuri’ar amma Rasha ta yi amfani da kujerarta wajen dakile yunkurin duk da matakin Amurka na kafiya don tabbatar da ganin an yi tir da Moscow.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp