Home DUNIYA Buhari: Nijeriya na fatan yin Aiki da Burtaniya

Buhari: Nijeriya na fatan yin Aiki da Burtaniya

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa Nijeriya na fatan yin aiki tare da sabon firaministan Burtaniya Rishi Sunak, a banagarori da dama da suka hadar da yaki da ta’addanci, samar da abinci gami da makamashi da tunkarara matsalar sauyin yanayi.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata takardar sanarwa da kakakin shugaban kasa Garba shehu ya fitar, mai taken kalaman shugaba muhammadu Buhari kan firamininsta burtaniya mai jiran gado, Rt Hon. Rishi Sunak MP.

Sanarwar take madadin gwamnatin tarayyar Nijeriya, dake matsayin babbar kasa cikin kasashe 21 na Nahiyar Afirka dake kkungiyar kasashe rainon Ingila ta commonwealth na yiwa Rishi Sunak maraba da shiga Ofishi.

“Matsayinsa na firaminista na farko daga jini biyu wato burtaniya da Asiya kuma mafi kankata a cikin shekaru 200, wannan zai kasance wani abin laka’akai ga matasa a cikin al’ummar mu biliyan 2.4 a kasashe 56 na Commonwealth”.

“A wannan muhimmayar rana, yana da kyau mu tuna da kyakkyawar alakar dake tsakanin kasashen mu Burtaniya da Nijeriya”.

Shugaban ya kara da cewa kungiyar kasashe renon ingila za ta tsaya tsayin daka wajen yakar ta’addanci tare da sabunta kudirorin ta na magance matsalar karancin abinci a duniya da ke haddasa tsadar rayuwa ga Al’ummomin duniya baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp