Home SIYASA Adeleke Ya karbi Rantsuwar Kama Aiki

Adeleke Ya karbi Rantsuwar Kama Aiki

An rantsar da Ademola Adeleke a matsayin sabon Gwamnan Jihar Osun, sakamakon nasarar da ya samu a zaben da akayi watannin da suka gabata.

Sabon gwamnan wanda nan take ya rufe asusun ajiyar jihar, ya bayyana aniyarsa ta bunkasa bangaren ilimi da tsaro da kula da lafiya da gina kayan more rayuwa, tare da sakin mara ga kananan hukumomi da kuma bangaren shari’a.

Adeleke ya kuma sanar da soke duk wasu nade naden da tsohon gwamnan yayi tun daga ranar 7 ga watan Yulin wannan shekara, cikinsu harda nada manyan sakatarorin gwamnati 30 da Oyetola yayi a makon jiya.

Sabon gwamnan ya kuma sauya sunan jihar daga ‘The State of Osun’ da ake kira, zuwa sunanta na assali, wato Jihar Osun.

Yayin bikin wanda ya samu halartar dan takarar shugaban kasar PDP Atiku Abukakar da gwamnonin jihohi da tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki, Gwamnan mai barin gado Adegboyega Oyetola yace ya barwa sabon gwamnan kundin da ya kai naira biliyan 14 a lalitar gwamnati.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp