Shugaban Najeriya Muhammadu ya Buhari ya bi sahun shugabannin ƙasashen duniya wajen miƙa saƙon ta’aziyyarsa kan rasuwar fitaccen ɗan ƙwallon duniya Edson Arantes do Nascimento wanda aka fi sani da Pele.
A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban ƙasar kan kafofin yaɗa labarai Malam Garba shehu ya fitar, shugaba Buhari ya bayyana ɗan wasan da cewa mutum ne ”mai kirki da ƙanƙan da-kai, duk da cewa shi babban ɗan wasa ne”.
Read Also:
”Pele ya gina kyakkyawar alaƙa tsakanin ƙasashe, da ƙabilu da ma addinai, haƙiƙa duniya ba za ta manta da shi ba”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Tsohon gwarzon ɗan wasan duniyar ya mutu ne ranar alhamsi bayan ya sha fama da rashin lafiya.
Ya lashe kofin duniya uku tare da zura ƙwallaye sama da 1,281, ya zama zaƙaƙurin ɗan wasan duniya.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1486 days 9 hours 4 minutes 3 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1468 days 10 hours 45 minutes 28 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com