Home General Kwalejin horas da jami’an ‘yan sanda ta Maiduguri ta yayi jami’ai 1180

Kwalejin horas da jami’an ‘yan sanda ta Maiduguri ta yayi jami’ai 1180

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya a ranar 29 ga watan Disamba 2022, ta yaye jumullar ‘yan sanda dubu daya da dari daya da tamanin (1180) daha kwalejin ‘yan sanda ta Maiduguri, dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nijeriya, ‘yan sandan na cikin wadanda sukayi nasara daga cikin ‘yan sanda dubu goma na shekarar 2021 da suka je atisayen daukar aikin.
Wannan na kushe ta ciki wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ASP Sani Kamilu Shatambaya, a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar Borno; sanarwar tace an gudanar faretin bikin yayi ‘yan sandan a lokaci guda a kwalejojin ‘yan sanda da ke fadin kasar inda aka kamala atisaye na tsawon watannin shida.
A yayin taron yaye ‘yan sanda an gabatar da kyaututtuka ga ‘yan sandan da dama da suka gudanar da abin yabawa.
Da yake jawabi a yayin taron babban sifeton ‘yan sandan Nijeriya Usman alkali baba Psc(+) NPM, fdc NEAPS, CFR wanda ya sami wakilcin mataimakin babban sifeton ‘yan sandan mai lura da sashen ‘yan sanda kwantar da tarzoma AIG ALI JANGA, ya bukaci sabbin ‘yan sanda dasu kasance masu gaskiya da Da’a wannan zai taimaka musu wajen cimma gaci a lokacinda suke gudanar da ayyukan su.
Sifeton janar din ya kuma bayyana cewa, za’a mayar da kananan ‘yan sandan zuwa kananan hukumominsu na asali domin cigaba da sanya dabarun ‘yansan na gwamnatin tarayya na mangace aikata gama-garin laifuka, tare da dakile aikata manyan laifukan a wuraren da aka turasu.
Kwamandan kwalejin DCP Bethrand Onuoha, da yake jawabin rufe taro, ya godewa babban sefeton ‘yan sandan Nijeriya, sannan ya bukaci sabbin ‘yan sanda dasu yi amfani da abinda aka koyar da su.
Kwamishinonin ‘yan sandan jihar Borno, Yobe da kuma Adamawa da kuma wasu manyan jami’an ‘yan sandan Nijeriya sun sami halartar taron yaye jami’an.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp