Home General NDLEA ta kama mutune 4 dauke da Cannivis Jakkuna 298

NDLEA ta kama mutune 4 dauke da Cannivis Jakkuna 298

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa reshen jihar kaduna ta sami nasara kame wasu da take zargin safarar miyagun kwayoyi dauke da jaka 298 na Cannabis Sativa.
Kwamandan hukumar na jihar Mista Ibrahim Braji ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai ranar laraba a jihar kaduna dake arewa maso yammacin Nijeriya.
Yace jami’an hukumar sun sami nasara kame wadanda ake zargi a yammacin ranar laraba a kauyen tasu mahuta a kan hanyar refinery, dake karamar hukumar chikun.
Yace sun kama wadanda ake zarne ne da suka hadar da maza 2 mata 2 dauke da cannabis mai nauyin kilogram dubu 3,576kg.
Yace ana gudanar da bincike kan lamarin domin gano sauran wadanda ke da hannu a safara, haka kuma rundunar ta sake fadada ayyukanta a jihar domin dakile ayyukan safarar miyagun kwayoyin.
Ya bayyana sabbin rashen hukumar da suka hadar da na makarfi, soba, kaduna North da kuma kaduna South, inda yacean kuma girke matocin sintiri a samara, zaria da sanga.
Braji ya kara da cewa kasancewar zaben 2023 na karatowa, hukumar zata shirya gangamin wayar da kan matasa matsalilin shan miyagun kwayoyi, da kuma matsalar sa agaresu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp