Home General Mayakan ISWAP Sun mika wuya a Jamhuriyyar Nijar

Mayakan ISWAP Sun mika wuya a Jamhuriyyar Nijar

Mayajan kungiyar tada kayar Baya na ISWAP da suka tsallake rijiya da baya, bayab harin da tsagin Boko Haram ya kai mu a Kayowa da Toumbun Gini, a Arewa maso gabshin yankin Tafkin Chadi, sun mika wuya hannun hukumomi a Tumour, ta Jamhuriyyar Nijar.
Zagazola ya ruwaito cewa mayakan ISWAP sun mika wuya a ranar 10 ga watan Janairu biyo bayan harin da abokan hamayyar su ta boko haram ke kai musu.

Harin ISWAP kan sansanin boko haram ya haifar da asarar rayuka tun a ranakun 31 ga Disamba da kuma 8 ga watan Janairun, 2023.
Harin kungiyar ta kai bisa jagorancin ABU UMAIMAH da akafi sanj da BAKOURA DORO, ya tarwatsa maboyar yan Ta’addan dake Toumbum Allura, Kurnawa, Kayowa da kuma Toumbun Gini, wanda ya tilastawa Abu Moussab al-Barnawi da wasu kwamandojin tsirewa.

Ci gaba da fafatawa tsakanin JAS da ISWAP dai da alama dai ba mai karewa ba ce ganin yadda yunkurin da kungiyoyin ke yi na hada karfi da karfe domin yakar sojojin Najeriya da na MNJTF ya gagara.

Dangane da wannan yanayin ne kungiyar ISWAP ke neman goyon bayan mayakan ISIS na kasashen waje da suka hadar da Mali, Burkina Faso da Somaliya don taimaka musu su karya JAS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp