Home General An sanya dokar hana fita a Jihar Niger

An sanya dokar hana fita a Jihar Niger

Gwamnatin jihar Niger ta sanya dokar ta baci biyo bayan kisan wani mai gari a jihar.
Gwamnan jihar Niger Abubakar Sani Bello ya sanay dokar hana zirga-zirga a kauyen
Lambata dake karamar hukumar Gurara, biyo bayan wata hatsaniya da tayi sanadiyyar hallaka wani mai rike da sarautar gargaji Mohammed Abdulsafur.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da sakataren Gwamnati jihar Ahmed Matane, ya fitar a ranar lahadi a Minna babban birnin jihar.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan daba sun hallaka dagacin Lamabata ne a ranar Asabar biyo bayan wata tarzoma.
Bello ya bada umarnin cewa

Dokar zata fara ne daga karfe 6:00am Zuwa 6:oopm farawa daga ranar Lahadi kuma har sai baba ta gani.
Ya kara da cewa an sanya dokar ne domin taimakawa jami’an tsaro su nemo bakin zaren matsalar, su tseratar da Rayukan Al’umma da dawo da doka da Odar.
Sanarwa ta kuma bayyana cewa Gwamnatin jihar tayi Allawadai da wannan tarzoma data auku a garin na lambata.
Ta kuma bukaci Al’ummar garin dasu bi doka domin baya jami’an tsaro damar dawo da zaman lafiya a garin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp