Home General NFIU ta magantu kan dokar haramtawa Gwamnoni cirar kudi a Asusun...

NFIU ta magantu kan dokar haramtawa Gwamnoni cirar kudi a Asusun Gwamnati

Hukumar tattara bayanan sirri kan harkokin kuɗi ta Najeriya ”Nigerian Financial Intelligence Unit” (NFIU) ta ce haramcin da take ƙoƙarin sanyawa kan cire kuɗi daga asusun gwamnatin tarayya da na jihohi abu ne da zai taimaka wa gwamnonin ba cutar da su ba.

Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar ta hannun jami’inta na hulda da jama’a Ahmed Dikko sa’o’i bayan ƙungiyar gwamnonin ƙasar ta soki sanarwa da hukumar ta fitar ranar 5 ga watan Janairu, ta umartar bankuna da su dakatar da bai wa gwamnoni kudaɗe daga asusun gwamnati daga ranar 1 ga watan Maris mai zuwa.

“Sabuwar dokar da hukumar NFIU ke shirin ƙaƙabawa game da sha’anin shige da ficen kuɗi baya cikin tsarin dokokin da ayyukan hukumar” Kamar yadda ƙungiyar gwamnonin ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

Ƙungiyar gwamnonin ta kuma kafa kwamiti mai mambobi shida da za su tattauna da babban bankin ƙasar domin duba batun matsalolin sha’anin harkokin kuɗi da ƙasar ke fuskanta.

A martanin da hukumar ta NFIU ta fitar ta ce a shirye take domin hada kai da kwamitin da ƙungiyar gwamnonin ta kafa domin wayar musu da kai game muhimmancin sabon kuɗurin.

”Sannan abun da muke ƙoƙarin aiwatarwa bai saɓa doka ba. Mun bayar da ƙa’idar ne domin magance tarin bincike da muka hango wa gwamnonin. Mun sanya ƙa’idar ce domin taimaka wa gwamnonin ba don cutar da su ko wani ma’aikacin gwamnati ba” kamar yadda sanarwar da NFIU ta fitar.

Sannan kuma hukumar ta ce a baya ta sanya makamanciyar wannan doka kan ƙananan hukumomi, inda aka kai ta kotu, amma kuma sai ta yi nasara a kotun.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp