Home General Hukumar zabe tace a shirye take wajen gudanar da zaben 2023

Hukumar zabe tace a shirye take wajen gudanar da zaben 2023

Shugaban Hukumar Zaben Najeriya Farfesa Mahmood Yakub ya ce za a gudanar da zabukan kasar da ke tafe kamar yadda aka tsara a wannan shekara ta 2023.

Yayin da yake jawabi a taron majalisar zartarwar kasar da Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta yau Laraba a fadar mulki da ke Abuja, Mahmood ya ce zaben shugaban kasa da ‘yan majalisar tarayya yana nan yadda aka tsara ranar 25 ga watan nan na Fabrairu.

Haka kuma shi ma zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi da za a yi ranar 11 ga watan Maris yana nan ba ja da baya kamar yadda aka tsara yi, in ji shugaban na INEC.

Shugaban hukumar zaben ya bayyana gaban majalisar ne yayin da ya rage kwana 17 a fara zabukan, domin ya yi bayani kan halin da ake ciki game da shirye-shiryen hukumarsa.

Da yake zantawa da manema labarai bayan fitowa daga zauren majalisar, Farfesa Yakubu ya ce ya bayyana ne gaban majalisar ministocin domin sanar da ita irin shirin da hukumar ta yi na gudanar da manyan zabukan na bana.

Ya kara da cewa daman abin da aka saba yi ne a duk lokacin da ake daf da zabe a kasar, shugaban hukumar ya yi wa majalisar zartawa bayani inda shirye-shiryen suka kwana.

Sai dai akwai wasu matsaloli guda uku da a baya hukumar ta ce ka iya yin tarnaki ga gudanar zabukan, matsalolin da suka kunshi rashin tsaro da karancin takardun kudi da kuma man fetur.

Ko baya ga yin wannan bahasin gaban majalisar ministocin, ana sa ran shugaban hukumar zaben ya sake bayyana gaban majalisar magabata ta kasa wato Council of State ranar Juma’a, domin sanar da ita a hukumance irin yadda hukumarsa ta kintsa domin gudanar da manyan zabukan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp