Home General ASUU ta soki Gwamnatin tarayya bisa Karancin Man Fetur

ASUU ta soki Gwamnatin tarayya bisa Karancin Man Fetur

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta soki gwamnatin tarayya kan ƙarancin Kuɗi da na man fetur da ake fama da shi a faɗin ƙasar.

Wannan na kunshe ta ciki wata sanarwa da shugaban ƙungiyar Emmanuel Osodeke ya fitar ya ce gwamnatin ƙasar a matakan tarayya da jihohi da kuma ƙananan hukumomi na aiwatar da tsare-tsaren da suke wahalar da talakawan ƙasar.

Ya ƙara da cewa matakin da Kotun Ƙolin ƙasar ta ɗauka na dakatar da aiwatar da wa’adin 10 ga watan Fabrairu na daina amfani da tsofaffin takardun kuɗi, zai taimaka wajen sauƙaka wa ‘yan ƙasar halin matsin da suke ciki.

Mista Osodeke ya ƙara da cewa tsarin da gwamnan CBN Godwin Emefiele ya ɓullo da shi na ”hana walwalar kuɗi” an taɓa yin sa a Indiya a shekarar 2016 wanda ya haifar da wahalhalu a ƙasar.

“Dan haka, ASUU tana yaba wa Kotun Ƙoli da wannan hukunci ta hanyar la’akari da halin da talaka ke ciki wanda Emefiele ya jefa su ciki”, in ji Osodeke.

A makon da ya gabata ne dai Kotun Kolin ƙasar ta dakatar da Babban Bankin ƙasar aiwatar da wa’adin 10 ga watan Fabrairu na daina amfani da tsoffin kuɗin, bayan da wasu jihohin ƙasar uku suka shigar da ƙara gaban kotun.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp