Home General Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin...

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin ƙasar

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin ƙasar gabanin babban zaɓen ƙasar da ke tafe ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga watan Maris da ke tafe.

Ministan Ilimin ƙasar Adamu Adamu ne ya sanar da haka cikin wata wasiƙa da jami’in ma’aikatar I.O Folorunsho ya sanya wa hannu, tare da aike wa babban sakataren hukumar kula da kwalejojin fasaha na ƙasa (NBTE) Idris Bugaje.

Ministan ya umarci shugabannin makarantun duka kwalejojin fasaha cewa a tsadar da karatu daga 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris.

Wasiƙar ta ci gaba da cewa ”Sakamakon fargabar da ake da ita kan tsaron tsaron malamai da ɗalibai da kadarorin makarantunmu, Ministan Ilimi Adamu Adamu bayan tuntuɓa mai zurfi da hukumomin tsaro, ya bayar da umarnin rufe duka makarantun fasahar”

”Dan haka za a rufe makarntun daga ranar Laraba 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris 2023,”

A makon da ya gabata ne dai Hukumar Kula da Jami’o’i ta Najeriya ta bayar umarnin a rufe dukkanin jami’o’in ƙasar tsawon lokacin da za a gudanar da babban zaɓen ƙasar na 2023.

A wata sanarwar mai ɗauke da sa hannun mataimakin shugaban hukumar, mai kula da harkar gudanarwa, Chris J. Maiyaki, ya ce za a rufe jami’o’in ne domin kare lafiyar ma’aikata, da ɗalibai a tsawon lokacin zaɓen.

Bayanin ya ce umurnin ya fito ne daga ministan ilimi na Najeriyar, Adamu Adamu, inda aka umurci dukkanin shugabannin jami’o’i su rufe daga 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp