Home General farashin man fetur ya ƙaru a Nijeriya da kashi 55 a watan...

farashin man fetur ya ƙaru a Nijeriya da kashi 55 a watan Janairu -NBS

Hukumar kididdiga ta Najeriya ta ce farashin man fetur ya ƙaru da kashi 55 a watan Janairu.

Wannan na kunshe ne cikin wani rahoto da hukumar ta fitar, inda ta ce a watan na Janairu, ‘yan Najeriya sun biya N257.12 a kan kowace lita.

Rahoton ya nuna cewa farashin a watan Janairun 2023 ya ƙaru da kashi 54.52 cikin 100 da kuma karuwar kashi 24.70 a kowane wata.

NBS ta kuma bayyana cewa jihar Imo ce ta fi kowace a sayar da litar man fetur, inda na ta ke a kan N332.14, sai Rivers a kan N327.14 da kuma Akwa-Ibom a kan N319.00.

Ta kuma lura da cewa Sokoto ce jihar da aka fi sayar da man fetur a kasan farashi, inda man fetur ɗin ke a kan N191.43 kan kowace lita, sai Filato a kan N192.14 da kuma Borno a kan N193.91.

‘Yan Najeriya da dama na ci gaba da biyan sama da N185 kan kowace lita da aka amince da shi a matsayin farashin man fetur sakamakon ƙarancin mai, kamar yadda rahoton hukumar kididdiga ta kasa ya nuna.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp