‘Yan takarar shugabancin Najeriya 18 sun sanya hannu a kan yarjejeniyar amincewa da sakamakon zaben 2023

‘Yan takarar shugabancin Najeriya 18 sun sanya hannu a kan yarjejeniyar amincewa da sakamakon zaben da za a yi ranar Asabar 25 ga watan nan na Fabarairu 2023.

Bisa tanadin yarjejeniyar, dukkanin ‘yan takarar sun amince cewa idan har ya kasance suna da wani ƙorafi kan zaɓen to za su bi hanyoyin da tsarin mulki ya tanada domin bi musu kadi.

Yarjejeniyar da aka yi a Abuja ranar Larabar nan wadda Kwamitin Zaman Lafiya na ƙasar ya shirye ta samu halartar dukkanin ‘yan takarar 18, tare da Shugaba Muhammadu Buhari, wanda za a gada.

Haka kuma tsohon shugaban ƙasar Kenya Uhuru Kenyata wanda shi ne jagoran masu sanya ido a zaɓen na Ƙungiyar Tarayyar Afirka, AU, da tsohon shugaban Afirka ta Kudu Thabo Mbeki duk sun halarta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com