Home General zaben 2023- NRC ta dakatar zirga-zirgar Jiragen kasa a Nijeriya

zaben 2023- NRC ta dakatar zirga-zirgar Jiragen kasa a Nijeriya

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Najeriya za ta dakatar da sufurin jiragen ƙasa a faɗin ƙasar na wucin-gadi gabanin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

Wannan na kunshe ta cikin watar  sanarwar da hukumar ta fitar mai ɗauke da sa-hannun mataimakin daraktan yaɗa labarai na hukumar Yakub Mahmood.

sanarwa tace hanyoyin jiragen ƙasan da dakatarwar za ta shafa sun haɗa da Abuja zuwa Kaduna da Warri–Itakpe da Lagos–Ibadan, da kuma hanyar Iddo Lagas-Ijoko.

Haka ta ce ta ɗauki matakin ne domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su gudanar da zaɓukan dake tafe ‘yan kwanaki masu zuwa.

Sanarwar ta kara da cewa Dakatarwar wucin-gadin za ta fara ne daga ranar 25 zuwa 27 ga watan Fabrairun da muke ciki, kamar yadda yake kunshe cikin sanarwar da hukumar ta fitar.

“Haka kuma, hukumar na sanar da al’umma cewa za a maido da zirga-zirgar jiragen ƙasan daga ranar Talata 28 ga watan Fabrairu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp