Home General An kama mutumin da ya lashi takobin hana gudanar da zabe a...

An kama mutumin da ya lashi takobin hana gudanar da zabe a Najeriya

Jami’an ‘yan sandan Finland sun cafke Simon Ekpa, wani mai rajin kafa kasar Biafra wanda kuma ya sha yin barazanar hana gudanar da zaben 2023 a Najeriya.

Ekpa ya jima yana furta kalaman tunzuri domin haddasa tashin hankali a Najeriya daga can mazauninsa a na kasar Finland.

Ekpa ya sha yin kira ga mutanen yankin kudu maso gabashin Najeriya da su rika mutunta umarnin Kungiyar IPOB na zaman gida kan tilas a kowanne mako, abin da ya kara fito da manufarsa ta neman raba kan Najeriya.

Kafin cafke shi a wannan Alhamis, gwamnatin Najeriya ta rattaba hannu kan wata takardar korafi domin ganin an cafke mutumin da ke goyon bayan ballewar kabilar Igbo daga kasar.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp