Home General Kotu ta bai wa INEC damar sake saita na’urar BVAS bayan karar...

Kotu ta bai wa INEC damar sake saita na’urar BVAS bayan karar PDP da LP

Kotun daukaka kara a Najeriya ta bai wa hukumar INEC izinin sake saita na’urar zabe ta BVAS da aka yi amfani da ita yayin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisu da ya gudana a ranar 25 ga watan da ya gabata.

Yayin zaman kotun na ranar laraba a Abuja fadar gwamnatin Najeriya, zaman da ya gudana karkashin jagorancin alkalai 3 da suka hadar da mai shari’a Joseph Ikyegh da ya karanto hukuncin kotun wanda ya sahalewa INEC saita na’urar ta BVAS gabanin zaben gwamnoni da ‘yan Majalisun jihohi da ke tafe a karshen makon nan.

Kotun ta umarci INEC ta nadi bayanan da ke cikin na’urar ta BVAS tare da adana su a waje mai tsaro baya ga sanya kwafi a rumbunan adana bayananta.

Kafin hukuncin na yau dai, Kotu ta baiwa  dan takarar jam’iyyar adawa ta PDP wato Atiku Abubakar da Peter Obi na jam’iyyar LP damar gudanar da bincike kan na’urar da sauran kayakin zabe masu muhimmanci don samun hujjojin da suke ikirarin an tafka magudi a babban zaben kasar.

‘Yan takarar jam’iyyun adawar da suka zo na biyu da na uku a zaben shugaban kasar na Najeriya wanda Bola Ahmed Tinubu ya yi nasara, sun bukaci isa ga na’urorin zaben ne don tattara hujjoji bayan shigar da karar da ke kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar.

Sai dai bayan izinin isa ga na’urorin da kotun sauraren karakin zaben Najeriya ta bai wa ‘yan takarar jam’iyyun adawa, INEC ta daukaka kara kan hukuncin bisa kafa hujjoji da illar da hakan zai yi ga zaben Gwamnoni da ke tafe.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp