Dan takarar gwamnan jihar Kano ƙarƙashin jam’iyyar ADP Sha’aban Ibrahim Sharada ya taya zaɓaɓɓen gwamna jihar Abba Kabir Yusuf murnar lashe zaɓe.
Read Also:
A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa Facebook, Sha’aba Sharaɗa ya yaba wa hukumar INEC da cewa ta yi abinda ya kamata.
Da safiyar ranar Litinin ne hukumar zaɓen jihar ta ayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan samun ƙuri’u mafi rinjaye.
Sha’aban Ibrahim Sharada na jam’iyyar ADP ya samu ƙuri’a 9,402 a zaɓen da aka gudanar.
PRNigeria hausa