• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home SIYASA Fadar Shugaban Kasa ta yi Martani Kan Batun Mika Mulki ga Tinubu
  • SIYASA

Fadar Shugaban Kasa ta yi Martani Kan Batun Mika Mulki ga Tinubu

By
Prnigeria
-
March 24, 2023
Tinubu and Buhari
Arewa Award

Fadar Shugaban Kasa ta yi Martani Kan Batun Mika Mulki ga Tinubu

 

Garba Shehu ya ce shirin gwamanatin Buhari na mika mulki ga shugaban kasa mai jiran gado, Bola Tinubu, ya yi nisa.

Mai magana da yawun shugaban kasar ya bayyana haka a wani martani kan batun da ke yawo a kafafen sadarwa cewa Buhari ba shi da niyyar mika mulki ga Tinubu.

Shehu ya kara da cewa Buhari ya kosa ya bar fadar shugaban kasa ya kuma koma mahaifarsa a Daura, da ke jihar Katsina.

Gidan Gwamnati, Abuja – Fadar shugaban kasa a ranar Juma’a, 24 ga watan Maris, ta karyata rahotannin da ke cewa Shugaba Muhammadu Buhari ba shi da niyyar mika mulki ga zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, a karshen wa’adin mulkinsa ranar 29 ga watan Mayu.

Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Garba Shehu ya fitar ya ce, tuni shirin gwamnati na mika mulki ya yi nisa, a cewar rahoton gidan talabijin na Channels.

Wani bangaren sanarwar ya ce:

”Fadar shugaban kasa na son sanar da cewa labarin karya ne kuma mara makama, ta kuma yi Allah wadai da jingina kalaman karya ga shugaba Muhammadu Buhari da kuma yada shi.

‘Ta ya zaka tallata wani iya karfinka, ka zabe shi sannan ace ba za ka mika ma sa mulku ba? Wannan tunanin marasa ilimi ne.”

Read Also:

  • Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota
  • NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta
  • Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda

Shehu bayyana kafar yada labaran da ta wallafa rahoton (ba Legit.ng ba) a matsayin ”mara sanin ya kamata” ya kara da cewa mammalakinta ”ya dauki bangare a siyasa, hasalima ya fadi a zaben shugaban kasa.”

Daga Buhari zuwa Tinubu: Fadar Shugaban kasa ta yi bayanin shirin mika mulki

Shehu kuma cigaba da cewa a kafa kwamitin mika mulki, da ya hadar da wakilan gwamnatin Buhari da kuma gwamnati mai jiran gado ta Tinubu.

A cewarsa, kwamitin na tattaunawa kullum.

”Tuni gwamnati ta fara shirin mika mulki. Kwamitin mika mulki, da ya hadar da wakilan gwamnati mai barin gado da mai jiran gado su na tattaunawa kusan kullum don shirya yadda za a mika mulki ga gwamnatin Tinubu/Shettima,” in ji shi.

”Akwai kananan kwamitoci 13 da aka fitar daga babban kwamitin, wasu, don shirya faretin sojoji da kuma raka shugaba Buhari, sun fara aikinsu ko su na daf da farawa. Zuwa yanzu, komai na tafiya dai dai kuma ba alamun tangarda.”

Buhari ya matsu ya koma Daura, in ji Shehu

Shehu ya kuma bayyana cewa shugaban kasar ya kosa ya koma garinsu Daura, da ke Jihar Katsina, don more hutun barinsa aiki.

Ya ce al’ummar Daura sun fara shirye shiryen tarbar dan su bayan ”kammala mulkinsa cikin nasara har na wa’adi biyu tsahon shekara takwas.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • buhari
  • Garba Shehu
  • Tinubu
Previous articleHukumar NITDA ta Gabatar da Satifiket ga Matan da Suka Samu Horo Kan Fasahar Zamani
Next articleHatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Babu sauran sakaci a jam’iyyarmu ta PDP – Kabiru Turaki

Tinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniya

Ban koma jam’iyyar APC ba – Namadi Sambo

Barau ya nada shugaban kungiyar zago akida na Kano mukami

Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Gwamnoni ku dauki aniyar hidimtawa Al’umma – buhari

Atiku ya yi martani kan kalaman Akume ga ‘yan Arewa

An sake zaɓar Okonjo-Iweala shugabar WTO a wa’adi na biyu

Dalilin Ndume na sa alamar tambaya kan gaggawar amincewa da ƙudurin haraji na Tinubu

Yahaya Bello ya musanta zargin rashawa a gaban kotu

Hukumar EFCC ta ce ta yi nasarar kama Yahaya Bello

PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen jihar Ondo

Recent Posts

  • Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota
  • NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta
  • Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda
  • Kotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yari
  • Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1642 days 5 hours 11 minutes 38 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1624 days 6 hours 53 minutes 3 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin MotaNNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar DeltaKotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam SandaKotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yariHar yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso - TuggaNajeriya ta ce jirgin ta ya yi saukar gaggawa ne a Burkina FasoBurkina Faso ta tsare jirgin sojin Najeriya kan keta sararin samaniyar ƙasarKwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin NijeriyaAn ceto wasu daga cikin daliban da aka sace a makarantar Papiri da ke jihar NejaAmnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi MagajiAkwai sa hannun 'yan siyasa a kamen da aka yiwa Muhuyi - Gwamnatin KanoMajalisa ta amince da naɗin Chris Musa ministan tsaron NajeriyaWadanda aka sace a Cocin jihar Kwara sun shaki iskar 'yanciGwamnatin Nasarawa za ta kafa ƴan sandan JihaGwamnan Osun Ademola Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP
X whatsapp