Home SIYASA Ku dakata da bai wa gwamnatin Kano bashi- Abba Gida-gida

Ku dakata da bai wa gwamnatin Kano bashi- Abba Gida-gida

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya shawarci masu bai wa gwamnatin jihar bashi da cewa su dakata.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran sabon zaɓaɓɓen gwamnan Sunusi Bature Dawaki Tofa ya fitar, inda tace sabon gwamnan ya shawarci masu bai wa gwamnatin jihar bashi na cikin gida da na waje da kada su amince da bai wa gwamnatin jihar bashi daga ranar 18 ga watan Maris zuwa ranar 29 ga watan Mayu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa sabuwar gwamnatin ba za ta yi la’akari da bashin da jihar ta karɓa, ba tare da saninta ba daga ranar zaɓe zuwa ranar da aka rantsar da sabuwar gwamnatin.

Haka kuma sanarwar ta ce masu bin gwamnatin jihar bashi a yanzu su kwana da sanin cewa za a sake nazarin ƙa’idojin bashin bayan kammala bincike a kan kowanne bashi da ake bin jihar.

Ko a makon da ya gabata ma sabon zaɓaɓɓen gwamnan ya bayar da shawara ga masu gine-gine a filayen gwamantin jihar da su dakatar da ayyukansu.

To sai dai ‘yan kwanaki bayan shawarar zaɓaɓɓen gwamnan, gwamnan jihar mai barin gado Abdullahi Umar Ganduje ya mayar masa da martani, yana mai cewa sabon gwamnan ya yi haƙuri, ya daina fitar da sanarwar hukuma da sunan shawara ga jama’a.

duk da cewa ana kallon martanin na Gandujen ka iya zama musayar yawu tsakanin Gwamnatin mai ci da mai barin gado.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp