Home SIYASA zaben 2023: APC ta Maka Abba gida-gida gaban Kotu

zaben 2023: APC ta Maka Abba gida-gida gaban Kotu

Jam’iyyar APC reshen jihar Kano da ke Najeriya ta shigar da kara a gaban kotun sauraren korafe-korafen zaben gwamna, inda take kalubalantar Hukumar Zaben Kasar ta INEC kan yadda ta ayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

Jam’iyyar ta APC ta ce, Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida-Gida bai cancanci tsayawa takara a zaben ba saboda a cewarta, sunansa ba ya cikin jerin sunayen mambobin jam’iyyar NNPP ta aika wa INEC.

Kazalika APC ta yi zargin cewa, NNPP ba ta lashe zaben ba musamman ganin yadda aka kidaya wa jam’iyyar hatta kuri’un da suka lalace a cewarta, kuma tana ganin cewa, da an cire lalatattun kuri’un, da ita za ta yi nasara.

Koda yake, dan takarar gwamnan na jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna bai yi tarayya da jam’iyyar ba wajen shigar da wannan koken.

Tuni dai Gawuna ya amince da shan kayi a zaben wanda sakamakonsa ya nuna cewa, Abba Gida-Gida ya samu kuri’u miliyan 1 da dubu 19  da 602, yayin da shi kuma ya samu kuri’u dubu 890 da 705.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp