Home SIYASA zaben 2023: APC ta Maka Abba gida-gida gaban Kotu

zaben 2023: APC ta Maka Abba gida-gida gaban Kotu

Jam’iyyar APC reshen jihar Kano da ke Najeriya ta shigar da kara a gaban kotun sauraren korafe-korafen zaben gwamna, inda take kalubalantar Hukumar Zaben Kasar ta INEC kan yadda ta ayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

Jam’iyyar ta APC ta ce, Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida-Gida bai cancanci tsayawa takara a zaben ba saboda a cewarta, sunansa ba ya cikin jerin sunayen mambobin jam’iyyar NNPP ta aika wa INEC.

Kazalika APC ta yi zargin cewa, NNPP ba ta lashe zaben ba musamman ganin yadda aka kidaya wa jam’iyyar hatta kuri’un da suka lalace a cewarta, kuma tana ganin cewa, da an cire lalatattun kuri’un, da ita za ta yi nasara.

Koda yake, dan takarar gwamnan na jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna bai yi tarayya da jam’iyyar ba wajen shigar da wannan koken.

Tuni dai Gawuna ya amince da shan kayi a zaben wanda sakamakonsa ya nuna cewa, Abba Gida-Gida ya samu kuri’u miliyan 1 da dubu 19  da 602, yayin da shi kuma ya samu kuri’u dubu 890 da 705.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp