Home DUNIYA IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba wajen samun bunkasar...

IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba wajen samun bunkasar tattalin arziki.

Asusun Lamuni na Duniya, wato IMF ya fitar da sabon rahoto na ‘Hasashen Tattalin Arzikin’ kasashen duniya na shekarar 2023 da na 2024.

A cikinsa, IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba a samun bunkasar tattalin arziki, da karin kashi 3.2% a ma’aunin GDP.

Nijeriya tana rukunin sabbin kasuwanni ko masu tattalin arzikin mai tasowa, inda take ta uku, da kashi 3.2%, sai ta biyu, China da kashi 5.2%, sai kuma Indiya da ta kasance ta daya, da kashi 5.9.

Idan aka duba cikin kasashen da ke Kudu da Sahara, yankin da ake yi wa kallon yana cikin mafi karancin ci gaba, Nijeriya ta doke Afirka ta Kudu wadda ke da kashi 0.1% kacal a 2023.

Pierre-Olivier Gourinchas, shi ne babban jami’in tattalin arzikin na IMF, yayin gabatar da rahoton, ya bayyana cewa tattalin arzikin duniya yana farfadowa duk kuwa da kangin da bankuna suka shiga a baya-bayan nan.

Sabon rahoton ya fitar da wani jadawali na jerin sauye-sauyen farashin kayayyakin amfanin jama’a, da za a samu a wannan shekara a kasashen duniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp