Doguwa/Tudun Wada: Hukumar INEC ta Bai wa Alhassan Doguwa Shaidar Sake Cin Zaɓe a Matsayin ɗan Majalisar Wakilai
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe a matsayin ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Doguwa da Tudun Wada, daga Jihar Kano.
Read Also:
Karo na shida kenan, da Ɗan Majalisar na tarayya ke samun nasarar zuwa majalisar ta wakilai daga Jihar Kano, da ke Arewa Maso Yammacin Najeriya, tun bayan dawowar mulkin dimokraɗiyya a Najeriyar a cikin shekarar 1999.
Tun da farko dai hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙara (INEC) ta soke nasarar Da Hon. Alhassan Ado Doguwa ya samu, a zaɓen 25 ga watan Fabrairu, saboda jami’in sanar da sakamakon, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya ce “tursasa masa” aka yi.
Sai dai, jami’in sanar da sakamakon a zaɓen cike-giɓi na mazaɓar, Farfesa Sani Ibrahim a ranar 15 ga watan Afrilu, ya bayyana Alhassan Doguwa Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara da ƙuri’u 41,572 bayan wannan zaɓen lafiya.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1485 days 14 hours 26 minutes 42 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1467 days 16 hours 8 minutes 7 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com