An wayi gari da karar harbe-harbe a Khartoum

An shiga mako na biyu ana gwabza yaki a Sudan tsakanin sojojin kasar da kuma rundunar RSF, a daidai lokacin da wa’adin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimmawa yazo karshe.

Harbe-harbe da karar fashewar bama-bamai sun lafa sai dai an wayi garin Asabar da karar harbe-harbe, wanda hakan alama ce ta rugujewar yarjejeniyar da aka cimmawa ta tsagaita wuta.

Duka bangarorin biyu dai sun ta ikirarin cewa za su tsagaita wuta sai dai abin ya ci tura.

Fiye da mutane 400 ne suka mutu yayin da dubbai suka jikkata tun bayan da fada ya kaure ranar Asabar tsakanin rundunar soji karkashin jagorancin babban hafsan soji Abdel Fattah da mataimakinsa, Mohamed Hamdan Daglo da aka fi sani Hemeti, wanda ke shugabantar rundunar (RSF).

Ranar Juma’a rundunar sojin ta sanar cewa ta “amince ta tsagaita wuta ta kwana uku” domin “bai wa ‘yan kasar damar yin bikin karamar Sallah da kuma bari a kai kayan agaji”, kamar yadda Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres da Sakataren Wajen Amurka Antony Blinken suka bukaci a yi.

Ganau a yankuna da dama na Khartoum sun ce an kwashe tsawon Juma’a ba tare da jin karar harbe-harbe da luguden wuta ba.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 54 minutes 36 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 36 minutes 1 second

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com