Home SIYASA Sanata Godswill Akpabio ya zama shugaban majalisar dattijai ta goma

Sanata Godswill Akpabio ya zama shugaban majalisar dattijai ta goma

Sanata Godswill Akpabio ya yi nasarar zama Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya ta goma, bayan zaɓaɓɓun ‘yan majalisar dattijai sun kaɗa ƙuri’a.

Akawun majalisar tarayya, Sani Tambuwal ne ya bayyana sakamakon zaɓen da ‘yan majalisar suka yi, inda ya ce Sanata Godswill Akpabio ya yi nasara da rinjayen ƙuri’a 63.

Ya dai kayar da abokin fafatawarsa, Sanata Abdul’aziz Yari ne wanda ya samu ƙuri’a 46.

Tuni Akawu Sani Tambuwal ya rantsar da sabon Shugaban Majalisar Dattijan, bayan ƙuri’un da ‘yan majalisa 107 suka kaɗa da safiyar Talata.

Matakin ya zo ne jim kaɗan da buɗe zaman majalisa ta goma a ranar Talata.

Magoya bayan sabon shugaban majalisar dattijan sun yi ta sowa a zauren majalisar inda suka je suna rungume Sanata Godswill Akpabio.

Da kammala zaɓen sabon shugaban majalisar dattijain kuma, yanzu an shiga matakin zaɓen mataimakinsa, inda Sanata Godswill Akpabio ya ɗare kan kujerar shugaban majalisar dattijai

Akawun Majalisar Dattijai ya ayyana Sanata Barau Jibrin a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattijai ta goma

Daga bisani, akawun majalisa ya rantsar da Sanata Barau Jibrin a matsayin halastaccen mataimakin shugaban majalisar dattijai.

Akpabio da Barau su ne ‘yan takarar da jam’iyyar APC mai mulki da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suka mara wa baya don zama shugaban majalisar dattijai da mataimakinsa.

Tuni dai, akawun majalisar dattijai ya shiga rantsar da zaɓaɓɓun ‘yan majalisar dattijan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp