Tajudden Abbas ya zama kakakin majalisar wakilai ta goma

Dan majalisar tarayya mai wakiltar Zaria Hon Tajudden Abbas ya lashe zaben da akayi na shugabancin majalisa ta goma wanda ya gudana lokacin kaddamar da majalisar wakilan a talatar nan.

Dan majalisa Abbas na Jam’iyyar APC wanda kuma shine dantakarar fadar shugaban kasa, ya lashe zaben ne da kuri’u 353 inda yakayar da tsohon mataimakin shugaban majalisar wakilan data gabata Ahmed Idris wase wanda yasamu kuri’u 3.

Wanda yazo na uku Aminu Jaji Shima ya samu kuri’u 3 daga cikin kuri’u 359 da aka kada.

Tunda fari dai Mukhtar Betar, da Yusuf Gagdi, da Miriam Onuoha da kuma Sada Soli wadanda suka tsaya takarar sun janyewa Tajudden Abbas.

Kodayake an kai ruwa rana da Betara kafin daga bisani yamika wuya ya amince da janyewar.

Tsohon shugaban masu rinjaye kuma dan majalisa mai wakiltar Tudun Wada da Doguwa Hon Alhassan Ado Doguwa, shine wanda yafara hakura da burinsa na shugabantar majalisar ta goma.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 12 hours 1 minute 35 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 43 minutes 0 second

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com