Bazoum ya Nemi agajin Amurka

Hamɓararren shugaban Nijar ya roƙi Amurka da “duka ƙasashen duniya” da su taimaka “wajen mayar da ƙasar kan tsarin Mulkin damukradiyya” bayan juyin mulkin da aka yi a makon jiya.

Cikin wata maƙala da ya rubuta a jaridar Washington Post, Shugaba Mohamed Bazoum, ya ce ya rubuta maƙalar ce a matsayin wadda aka yi “garkuwa” da shi.

Rashin kwanciyar hankali na ƙara ta’azzara a ƙasar da ke yammacin Afrika tun bayan hambarar da shugaban.

A ranar Alhamis, shugaban da ya jagoranci juyin mulkin ya sanar da kiran jakadunsu gida daga ƙasashen Faransa da Amurka da Najeriya da kuma Togo.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com