Home DUNIYA Gwamnatin Habasha ta saka dokar ta baci ta tsahon watanni 6

Gwamnatin Habasha ta saka dokar ta baci ta tsahon watanni 6

Gwamantin habasha ta saka dokar ta baci ta watanni shidda a yankin Amhara, yanki na biyu mafi gima a kasar.

Wannan na zuwa ne biyo bayan wasu arangama da ake tsakanin dakarun sojin kasar da wasu gungun mayaka, abinda ya haifar da dakatar da zirga-zirga.

Rikicin daya barke a yanki a wannan mako, ya zama babbar barazana ga tsaron kasar shekaru biyu bayan rikicin yankin Tigray wadda ke makotaka da Amhara.

Gwamantin yankin Amhara ta bukaci tallafin Karin jami’an tsaro daga gwamantin tarayyar kasar domin tabbatar da zaman lafiya.

Ta cikin wata sanarwa da ofishin friminista kasar Abiy Ahmad ya fitar yace, ya zame mana wajibi mu Sanya dokar ta bacin domin samar da tsaro kafin lamarin ya ta’azzara.

Habasha ce kasa ta biyu mafi yawan al’umma bayan Nijeriya, na fuskantar matsalar tashe-tashen hankula, tun bayan darewar Abiy Ahmad karagar mulkin kasar a shekarar 2018, duk da cewa ya sami lambar yabo ta zaman lafiya a shekarar 2019 bisa gudunmawar daya bayar wajen samar da zaman lafiya a kasar Eritrea.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp