Home DUNIYA Sojojin ECOWAS sun kagu su kaddamar da Matakin soji kan Jamhuriyar Nijar

Sojojin ECOWAS sun kagu su kaddamar da Matakin soji kan Jamhuriyar Nijar

Ƙasashen Yammacin Afrika sun amince da wani tsari na ɗaukar matakin soji kan Nijar, idan har sojojin da suka yi juyin mulki suka ƙi amincewa da sharaɗin dawo da hamɓarren shugaba, Mohamed Bazoum bisa karagar mulkin.

Tun da farko ECOWAS ta bai wa sojojin na jamhuriyar Nijar wa’adin ranar Lahadi su mayar da mulki ga farar hula.

Alamu na nuna cewa sojojin Ecowas sun ƙagu da su ƙaddamar da yaƙi a Nijar idan har hakan ya zama dole.

Yanzu haka dai, Najeriya ta rufe iyakokin ƙasar da Nijar, ta kuma yanke wutar da take bai wa Nijar din duk a lokaci guda, matakan sun haddasa tashin farashin kayan masarufi a ƙasar, hakan na nuna yadda matakan Ecowas ɗin za su haddasa wahalhalu ga ƴan ƙasar.

A ranar Alhamis wata tawaga ta kungiyar ta je Nijar, domin shiga tsakani sai dai ba ta samu damar ganawa da shugaban mulkin sojin ba, da ma hamɓararren shugaban na farar hula.

Masu aiko da rahotanni sun ce, ɗaukar matakin soji kan lamarin zai iya zama mai wahala sosai, saboda kayan aiki, da kuma hadari, domin zai iya kara dagula al’amura a yankin, wanda masu ikirarin jihadi ke yi wa ta’annati.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp