Home General Atiku ya yabawa Tinubu kan yaki da cin hanci da Rashawa

Atiku ya yabawa Tinubu kan yaki da cin hanci da Rashawa

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 da ya gabata na jam’iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya ce matakin dakatar da ministar jin ƙai da yaƙi da talauci, Betta Edu, abin yabawa ne,ko da yake bai isa ba.

Shugaba Tinubu ya dakatar da ministar ne a jiya Litinin kuma ya umarci hukumar EFCC ta gudanar da bincike a kanta, bayan ya fuskanci kiraye-kirayen a ɗauki mataki a kanta saboda zarge-zargen tafka almundahana, ko da yake ta musanta zarge-zargen.

Ministar da aka dakatar ta dai fuskanci gagarumar suka ne bayan kwarmata wasu takardun kashe kuɗi daga ma’aikatarta, waɗanda suka nuna ta bayar da umarni ga babbar akanta ta biya naira miliyan 585 cikin wani asusun ajiyar wata, lamarin da ake zargin ya saɓa ƙa’idojin kashe kuɗi na gwamnati.

A cikin wata wasiƙa da wani mataimakinsa na musamman Phrank Shaibu ya fitar, jagoran adawar Najeriya ya ce abin takaici ne ganin yadda shirin da aka kafa don tsamo ‘yan Najeriya miliyan 100 daga matsanancin talauci amma kamar yadda ake zargi ya zama saniyar tatsa ga gwamnatocin jam’iyyar APC.

Ya ce, “Ko da yake Tinubu ya cancanci yabo saboda dakatar da Betta Edu, amma mun yi imani, yunƙurin ya zo a makare. Da farko, ba shi da wata alaƙa ta naɗa ta a matsayin minista ta irin wannan muhimmiyar ma’aikata. Sai dai Tinubu ya fifita siyasa a kan ƙwarewa, lamarin da ya janyo wannan abin kunya.

Atiku wanda ya yi kira a yi wa ma’aikatar garambawul, ya kuma yi zargin cewa ba Betta Edu kaɗai ba ce da hannu a wannan badaƙala.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp