• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General Jan hankali ga ‘yan uwa ‘yan Kwankwasiyya
  • General

Jan hankali ga ‘yan uwa ‘yan Kwankwasiyya

By
Daga Nazeer A. Adam
-
February 11, 2024
Arewa Award

Bari na fara da tariya;

A lokacin da Allah ya karbi rayuwar Kakan mu, ma’ana mahaifin jagora Engr. Rabiu Musa Kwankwaso, Mai girma Majidadin Kano Alh. Musa Saleh, a cikin wadanda mukayi mamakin halartarsu Miller road domin yiwa Jagora gaisuwa akwai Mai martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero da sauran yan uwansa, duk da a al’ada ba mu saba ganin Sarkin kano yana zuwa ta’aziyya ba, wanda a lokacin dukkan mu da mukewa bin tsarin kwankwasiyya mun ji dadin wannan karamcin, kuma haka ya sanyayawa ran mu, da yawan mu munyi posting domin nuna jin dadin mu. WANNAN KARAMCI NE.

Ranar da Mai girma gwamna Alh. Abba Kabir Yusuf ya ziyarci fadar mai martaba sarkin kano a zagayen yakin neman zabe, kowa ya shaida irin Karamcin da Mai martaba Sarki ya nuna wa tawagar mu, wanda a wannan lokacin ma mun cika duniya muna fadin tarbar mutunci da mai martaba Sarki yai mana. ANAN MA AN MANA KARAMCI.

Me ya biyo baya?

Ranar da aka yi bikin rantsuwar mai girma gwamna a filin kwallon kafa na kofar mata, Mai martaba Sarkin kano Alh. Aminu Ado Bayero da Dan uwansa Sarkin Bichi Alh. Nasir Ado Bayero sun halarci taron rantsuwa, wanda a nan filin taro aka samu wasu suna jifa da ihu da nuna rashin da’a a garesu, wanda duniya ta ga yadda Jagora ya nuna fushinsa a wajen, wadda har sai da ta kai ga Jagora ya rako Sarki zuwa mota domin nuna baya tare da wannan rashin albarkar da wasu suka aikata, Amma su waye suka aikata haka ?? Ku biyo ni a gaba.

Read Also:

  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu

Ranar da Mai girma gwamna zai sake bude asibitin Hasiya Bayero wanda aka kwato daga hannun wasu marasa kishi, anan ma mai martaba Sarkin kano Alh.Aminu Ado Bayero ya halarci bikin bude asibitin, amma anan ma aka sake samun wasu suka aikata rashin da’a ta hanyar yiwa Sarki Ihu da kunna wakokin da zasu bakantawa Sarki. Wanda anan kowa yaga yadda Mai girma gwamna Alh. Abba kabir Yusuf ya leko ta saman mota yana nuna fushinsa ga matasan da suka aikata wannan rashin da’ar. Wanda daga baya hukumar yan sanda ya gabatar da bincike akan wannan marasa tarbiyyar, inda aka a cikin wadanda aka kama, an wallafa vedionsu a shafin mai magana da yawun hukumar yan sanda reshen jihar kano, kuma anan duniya ta shaida cewa wasu yara ne, masoyan Mai girma tsohon Sarkin kano Muhammadu Sunusi ne suke shiga rigar mu ta kwankwasiyya domin aikatawa sarkin kano Aminu rashin da’a.

A abubuwan nan da na jero guda hudu, ta bayyana a fili cewa Da Jagora da Mai girma gwamna basa goyon bayan yadda ake shiga rigar mu ta kwankwasiyya domin cimma wata manufa.

Tunda anyi walkiya, mun ga kowa, To WALLAHIL AZEEM lokacin da wasu marasa mutunci zasu cigaba da shiga rigar mu ta kwankwasiyya su aikata rashin da’a ya wuce, Ba zamu zuba ido ba, Mun dai na bari

Na san da yawa zasuyi mamakin fitowar kalaman nan daga bakina ko ??

To bari na sake jaddada muku, NI DAN KWANKWASIYYA NE CIKAKKE.

Idan kuma akwai wanda zai min gorin bawa kwankwasiyya gudunmawa, to Bismillah.

Sai kun jini a Karo na biyu.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 16 hours 16 minutes 54 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 17 hours 58 minutes 19 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Abba gida-gida
  • kwankwasiyya
  • Kwankwaso
Previous articleKaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya’
Next articleYadda ma’aikatan jinya da ungozoma suka gudanar da zanga-zanga a Abuja
Daga Nazeer A. Adam

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC

Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu

Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya

Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya – Dangote

Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a Zamfara

An samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari Mansur

Gwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Jirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga’

Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 ‘yan asalin Kano

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan ta’adda 60 a jihar Borno

An kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a Kano

Recent Posts

  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu
  • Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya
  • Bom ya kashe masu yawon murnar sallah a Sakkwato

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 16 hours 16 minutes 54 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1444 days 17 hours 58 minutes 19 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu - OPECTinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyyaA aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a ManguNajeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga SaudiyaBom ya kashe masu yawon murnar sallah a SakkwatoNan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya - DangoteSojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a ZamfaraAn samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari MansurGwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man feturJirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga'Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 'yan asalin KanoGwamnatin Tinubu ta jefa ƴan Najeriya fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci - NLCSojoji sun ce sun hallaka ƴan ta'adda 60 a jihar BornoAn kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a KanoRayuwar ƴan Najeriya na ƙara inganta - Tinubu
X whatsapp