• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General Jan hankali ga ‘yan uwa ‘yan Kwankwasiyya
  • General

Jan hankali ga ‘yan uwa ‘yan Kwankwasiyya

By
Daga Nazeer A. Adam
-
February 11, 2024
Arewa Award

Bari na fara da tariya;

A lokacin da Allah ya karbi rayuwar Kakan mu, ma’ana mahaifin jagora Engr. Rabiu Musa Kwankwaso, Mai girma Majidadin Kano Alh. Musa Saleh, a cikin wadanda mukayi mamakin halartarsu Miller road domin yiwa Jagora gaisuwa akwai Mai martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero da sauran yan uwansa, duk da a al’ada ba mu saba ganin Sarkin kano yana zuwa ta’aziyya ba, wanda a lokacin dukkan mu da mukewa bin tsarin kwankwasiyya mun ji dadin wannan karamcin, kuma haka ya sanyayawa ran mu, da yawan mu munyi posting domin nuna jin dadin mu. WANNAN KARAMCI NE.

Ranar da Mai girma gwamna Alh. Abba Kabir Yusuf ya ziyarci fadar mai martaba sarkin kano a zagayen yakin neman zabe, kowa ya shaida irin Karamcin da Mai martaba Sarki ya nuna wa tawagar mu, wanda a wannan lokacin ma mun cika duniya muna fadin tarbar mutunci da mai martaba Sarki yai mana. ANAN MA AN MANA KARAMCI.

Me ya biyo baya?

Ranar da aka yi bikin rantsuwar mai girma gwamna a filin kwallon kafa na kofar mata, Mai martaba Sarkin kano Alh. Aminu Ado Bayero da Dan uwansa Sarkin Bichi Alh. Nasir Ado Bayero sun halarci taron rantsuwa, wanda a nan filin taro aka samu wasu suna jifa da ihu da nuna rashin da’a a garesu, wanda duniya ta ga yadda Jagora ya nuna fushinsa a wajen, wadda har sai da ta kai ga Jagora ya rako Sarki zuwa mota domin nuna baya tare da wannan rashin albarkar da wasu suka aikata, Amma su waye suka aikata haka ?? Ku biyo ni a gaba.

Read Also:

  • Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100
  • Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban bara
  • Ana tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano – Gwamnati

Ranar da Mai girma gwamna zai sake bude asibitin Hasiya Bayero wanda aka kwato daga hannun wasu marasa kishi, anan ma mai martaba Sarkin kano Alh.Aminu Ado Bayero ya halarci bikin bude asibitin, amma anan ma aka sake samun wasu suka aikata rashin da’a ta hanyar yiwa Sarki Ihu da kunna wakokin da zasu bakantawa Sarki. Wanda anan kowa yaga yadda Mai girma gwamna Alh. Abba kabir Yusuf ya leko ta saman mota yana nuna fushinsa ga matasan da suka aikata wannan rashin da’ar. Wanda daga baya hukumar yan sanda ya gabatar da bincike akan wannan marasa tarbiyyar, inda aka a cikin wadanda aka kama, an wallafa vedionsu a shafin mai magana da yawun hukumar yan sanda reshen jihar kano, kuma anan duniya ta shaida cewa wasu yara ne, masoyan Mai girma tsohon Sarkin kano Muhammadu Sunusi ne suke shiga rigar mu ta kwankwasiyya domin aikatawa sarkin kano Aminu rashin da’a.

A abubuwan nan da na jero guda hudu, ta bayyana a fili cewa Da Jagora da Mai girma gwamna basa goyon bayan yadda ake shiga rigar mu ta kwankwasiyya domin cimma wata manufa.

Tunda anyi walkiya, mun ga kowa, To WALLAHIL AZEEM lokacin da wasu marasa mutunci zasu cigaba da shiga rigar mu ta kwankwasiyya su aikata rashin da’a ya wuce, Ba zamu zuba ido ba, Mun dai na bari

Na san da yawa zasuyi mamakin fitowar kalaman nan daga bakina ko ??

To bari na sake jaddada muku, NI DAN KWANKWASIYYA NE CIKAKKE.

Idan kuma akwai wanda zai min gorin bawa kwankwasiyya gudunmawa, to Bismillah.

Sai kun jini a Karo na biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Abba gida-gida
  • kwankwasiyya
  • Kwankwaso
Previous articleKaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya’
Next articleYadda ma’aikatan jinya da ungozoma suka gudanar da zanga-zanga a Abuja
Daga Nazeer A. Adam

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

‘Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026’

Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano – NHRC

Shugaban Najeriya zai iya dakatar da gwamna – Kotun Ƙoli

NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Kwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin Nijeriya

NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

KAROTA ta bukaci Al’ummar jihar Kano su bawa jami’anta hadin kai

Gwamnatin Neja ta ɗora alhakin sace ɗalibai kan makarantar

Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai

SAEMA 2025: IMPR Ta kaddamar da Littafi Kan Yaki da Sha da fatauci miyagun ƙwayoyi da fasa kwauri

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara karɓar harajin man fetur

Recent Posts

  • karo na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewa
  • Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100
  • Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban bara
  • Ana tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano – Gwamnati
  • JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1685 days 3 hours 6 minutes 27 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1667 days 4 hours 47 minutes 52 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
karo na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewaMatatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban baraAna tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano - GwamnatiJOHESU - Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma'aikatan asibitiGwamnan Kano zai koma Jam'iyyar APCGwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan SiyasaJam’iyyar NNPP ya yi martani kan fitar Gwamnan Kano daga NNPPGwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam'iyyar NNPPAmurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare KiristociShugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurkarahotannin daga jihar Katsina na cewa 'Yan bindiga sun kashe mutum 9 a jihar'Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026'Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe 74 ke fara aikiMayakan Boko Haram sun kutsa cikin ayarin sojin Najariya da bama-bamai a Borno
X whatsapp