Home DUNIYA Ana cigaba da Jimami a kasar Kenya bayan mutuwa babban Hafsan sojin...

Ana cigaba da Jimami a kasar Kenya bayan mutuwa babban Hafsan sojin kasar

Ana cigaba da zaman makoki na kwanaki uku a ƙasar Kenya don jimamin mutuwar babban hafsan hafsoshin tsaron kasar (CDF) Janar Francis Omondi Ogolla wanda ya mutu a wani jirgin sama da ya yi hatsari a lardin Elgeyo Marakwet da ke arewa maso yammacin kasar.

Ogolla, mai shekaru 61, ya mutu ne ranar Alhamis tare da wasu jami’an soji 9 da suka yi masa rakiya zuwa wani aiki na tantance yanayin tsaro a yankunan arewa maso yammacin Kenya da ke fama da matsalar rashin tsaro.

A wani jawabi da ya yi wa al’ummar kasar sa’o’i bayan hatsarin jirgin, shugaba William Ruto ya ce Kenya ta yi asarar “ɗaya daga cikin manyan hafsoshinta”.

Tsohon shugaban ƙasar Uhuru Kenyatta da jagoran ‘yan adawa Raila Odinga da jakadiyar Amurka Meg Whitman na daga cikin jagororin da suka yi ta’aziyyar mutuwar babban jami’in sojin na Kenya.

Marigayi Janar ɗin ya shiga rundunar sojojin Kenya (KDF) a shekara ta 1984 kuma ya kai matsayin babban kwamandan sojojin ƙasar a bara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp