Home General Gwamna Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashin N70,000 ga ma’aikatan Edo

Gwamna Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashin N70,000 ga ma’aikatan Edo

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya ƙara mafi ƙarancin albashin ma’aikatan gwamnati daga N30,000 zuwa N70,000 a jihar.

Gwamna Obaseki ya bayyana hakan ranar Litinin lokacin da yake ƙaddamar da ginin ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa reshen jihar.

A cewar gwamnan, sabon mafi ƙarancin albashin zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Mayu.

Matakin gwamnan na zuwa ne yayin da ƙungiyar ƙwadagon ke matsa wa gwamnatin tarayya lamba don ta ƙara mafi ƙarancin albashin domin rage wa ma’aikata raɗaɗin hauhawar farashi.

NLC da TUC sun nemi gwamnati ta mayar da mafi ƙanƙantar albashin ya zama N615,000.

Tun a watan Janairu ne gwamnatin Bola Tinubu ta kafa kwamitin mutum 37 da ke da wakilci daga ɓangarori da dama – gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu da ƙungiyar ƙwadago.

Kwamitin zai tattauna domin tsayar da mafi ƙarancin albashin da zai gabatar wa gwamnati domin amincewarta.

A lokacin ƙaddamar da kwamitin, mataimakin shugaban ƙasa, Kassim Shettima ya nemi kwamitin ya gaggauta wajen cimma matsaya, ya kuma miƙa rahotonsa da wuri.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp