Home General Kotu nada hurumin saurarar karar Dambarwar Masarautar Kano – Kotu

Kotu nada hurumin saurarar karar Dambarwar Masarautar Kano – Kotu

Babbar Kotun tarayya dake Jihar Kano a Arewacin Najeriya, ta ce tana da hurumin sauraron ƙarar da Alhaji Aminu Babba Ɗan agundi ya shigar akan batun dambarwar Masarautar Kano.
Kotun ƙarƙashin Jagorancin mai Shari’a Abdullahi Muhammad Liman tayi ƙwarya-ƙwaryar Hukuncin ne, biyo bayan inkarin da ɓangaren waɗanda ake ƙara suka yi na cewar kotun bata da hurumin sauraron ƙarar.
A zaman baya dai an tafka muhawara a tsakanin ɓangarorin biyu wato ɓangaren masu ƙara da waɗanda ake ƙara akan batun hurumin kotun dangane da Shari’ar, harma kotun ta ayyana yau Alhamis a matsayin ranar da zata bayyana matsayar ta akan batun hurumin.
Kuma tuni kotun ta ɗage zaman Shari’ar zuwa ranar 26 ga watan nan na Yuni domin ci-gaba da sauraron shariar bayan ta tabbatar cewa tana da hurumin sauraron ƙarar.
Ɓangaren Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ne dai suka shigar da ƙarar, a sakamakon rashin amince wa da matakin Gwamnatin Kano na rushe Masarautun jihar guda biyar bayan da Majalisar dokokin jihar tayi wa dokar Masarautun Garambawul.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp