Home General Kotu nada hurumin saurarar karar Dambarwar Masarautar Kano – Kotu

Kotu nada hurumin saurarar karar Dambarwar Masarautar Kano – Kotu

Babbar Kotun tarayya dake Jihar Kano a Arewacin Najeriya, ta ce tana da hurumin sauraron ƙarar da Alhaji Aminu Babba Ɗan agundi ya shigar akan batun dambarwar Masarautar Kano.
Kotun ƙarƙashin Jagorancin mai Shari’a Abdullahi Muhammad Liman tayi ƙwarya-ƙwaryar Hukuncin ne, biyo bayan inkarin da ɓangaren waɗanda ake ƙara suka yi na cewar kotun bata da hurumin sauraron ƙarar.
A zaman baya dai an tafka muhawara a tsakanin ɓangarorin biyu wato ɓangaren masu ƙara da waɗanda ake ƙara akan batun hurumin kotun dangane da Shari’ar, harma kotun ta ayyana yau Alhamis a matsayin ranar da zata bayyana matsayar ta akan batun hurumin.
Kuma tuni kotun ta ɗage zaman Shari’ar zuwa ranar 26 ga watan nan na Yuni domin ci-gaba da sauraron shariar bayan ta tabbatar cewa tana da hurumin sauraron ƙarar.
Ɓangaren Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ne dai suka shigar da ƙarar, a sakamakon rashin amince wa da matakin Gwamnatin Kano na rushe Masarautun jihar guda biyar bayan da Majalisar dokokin jihar tayi wa dokar Masarautun Garambawul.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp