Home AFIRKA Harin masu tada kayar baya a Mali ya kashe mutum 70 da...

Harin masu tada kayar baya a Mali ya kashe mutum 70 da jikkata wasu 200

Wani harin mayaƙa masu iƙirarin jihadi da aka kai sansanin horar da sojoji da filin tashi da saukar jiragen sama na babba birnin Mali, Bamako ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 70 tare da jikkata 200, adadi mafi muni na jami’an tsaro da aka taɓa samu a shekarun baya-bayann nan.

Wata majiyar tsaro da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa mutanee 77 ne suka mutu, kana 255 suka samu raunuka a harin da aka kai Bamako a ranar Talata.

Zalika, wani bayanin sirri na hukuma da aka tantance sahihancinsa ya ce adadin waɗanda suka mutu ya kai kimanin ɗari, inda ya bayyana sunayen 81 daga cikin su.

Jaridar Le Soir da ake wallafawa a kasar ta ranar Alhamis ɗin nan ya ruwaito cewa a ranar aka yi jana’izar kimanin dakaru masu karɓar soji kimanin 50.

Har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto mahukuntann gwamnatin sojin Mali ba su fitar da ainihin adadin waɗanda su ka mutu  a harin da ƙungiyar mayaƙa masu iƙirarin jihadi da ke da alaƙa da Al-Qaeda ta ɗauki alhakin kai wa ba.

Ƙwararru sun ce harin sshi ne naa farko irin sa a cikin shekaru, kuma ta yi mummmunan tasiri a kan gwamnatin sojin ƙasar.

Ba a cika samun hare-hare a babban birnin ƙasar Mali  kamar yadda ake samu a sauran sassan ƙasar kusan kullayaumin ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp