Home General Fararen hula 10,000 ne suka mutu a hannun sojojin Najeriya – Amnesty

Fararen hula 10,000 ne suka mutu a hannun sojojin Najeriya – Amnesty

Ƙungiyar kare hakkin ɗan’adam ta Amnesty International ta yi zargin cewa fararen hula kusan 10,000 ne suka mutu a hannun sojojin Najeriya, tun bayan fara yaƙi da ƙungiyar Boko Haram a arewa maso gabas.

Shugaban ƙungiyar ta Amnesty a Najeriya, Isa Sanusi, wanda ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Maiduguri, ya kuma zargi Boko Haram da sojoji da laifukan take ƴancin ɗan’adam.

A cewarsa, dakarun soji sun take ƴancin bil’adama yayin gudanar da ayyukansu a yankin na arewa maso gabas.

Ya nuna takaicinsa kan yadda sojoji suka musanta hannunsu a lamarin bayan gabatar musu da rahoton da Amnesty ta yi kafin ta fitar da shi ga jama’a.

Sanusi ya ce tuni ƙungiyar ta shigar da ƙara gaban Kotun Duniya da ke Hague, kan zargin take ƴancin ɗan’adam a arewa maso gabas.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp