• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General An saka ranar gudanar da gasar CHAN ta Afirka
  • General
  • WASANNI

An saka ranar gudanar da gasar CHAN ta Afirka

By
Bakoji
-
January 29, 2025
Arewa Award

Hukumar kula da kwallon kafa ta Afirka (CAF) ta tabbatar da ranar da za a buga gasar cin kofin nahiyar Afirka (CHAN) na shekarar 2024 da aka ɗage a baya.

Hukumar kwallon kafar Afirka ta bayyana cewa a yanzu za a gudanar da gasar ta CHAN daga ranar 2 ga watan Agusta zuwa 30 ga watan Agustan 2025.

Tun a watan Fabrairun 2025 ne aka shirya gudanar da gasar karo na takwas, wanda kasashen Kenya, Tanzania da Uganda za su dauki nauyin shirya gasar, amma an dage gasar saboda kalubalen samar da ababen more rayuwa da ingantattun wurare.

An tabbatar da sabuwar ranar da za a gudanar da gasar ne a yayin taron kwamitin zartarwa na CAF da aka gudanar a ranar Litinin a birnin Rabat na kasar Morocco, karkashin jagorancin shugaban CAF Dr. Patrice Motsepe.

Read Also:

  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu

Gasar ta CHAN ta keɓenta ne ga ‘yan wasan da ke taka leda a gasannin cikin gida, kuma Senegal ce ke rike da kambun gasar, bayan da ta lashe gasar karshe da aka yi a Algeria.

Kwamitin zartarwa na CAF ya kuma yanke shawara kan wasu gasanni masu zuwa, da kuma fara gasar cin kofin Afrika ta mata ta da za a yi a Morocco daga 22-30 ga Afrilu 2025.

Wadanda su ka kai wasan karshe a gasar za su samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta mata ta (FIFA Futsal) da za a yi a Philippines a cikin shekara.

An kuma amince da wani sabon tsari na neman tikitin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afrika na U-17 na shekarar 2025, inda adadin kasashen da ke halartar gasar ya karu daga 12 zuwa 16.

Kwamitin zartaswa ya kuma amince da fara tsarin bayar da damar karbar bakuncin gasa a nan gaba, ciki har da gasar zakarun Turai ta mata (2005, 2026 & 2027), U-17 AFCON (2026, 2027 & 2028), da U-20 AFCON (2027, 2029 & 2031).

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 4 hours 23 minutes 50 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 6 hours 5 minutes 15 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleECOWAS ta tabbatar da ficewar Nijar, Burkina Faso da kuma Mali a hukumance
Next articleGwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air
Bakoji

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC

Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu

Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya

Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya – Dangote

Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a Zamfara

An samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari Mansur

Gwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Jirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga’

Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 ‘yan asalin Kano

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan ta’adda 60 a jihar Borno

An kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a Kano

Recent Posts

  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu
  • Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya
  • Bom ya kashe masu yawon murnar sallah a Sakkwato

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 4 hours 23 minutes 50 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1444 days 6 hours 5 minutes 15 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu - OPECTinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyyaA aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a ManguNajeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga SaudiyaBom ya kashe masu yawon murnar sallah a SakkwatoNan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya - DangoteSojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a ZamfaraAn samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari MansurGwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man feturJirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga'Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 'yan asalin KanoGwamnatin Tinubu ta jefa ƴan Najeriya fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci - NLCSojoji sun ce sun hallaka ƴan ta'adda 60 a jihar BornoAn kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a KanoRayuwar ƴan Najeriya na ƙara inganta - Tinubu
X whatsapp