• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General An saka ranar gudanar da gasar CHAN ta Afirka
  • General
  • WASANNI

An saka ranar gudanar da gasar CHAN ta Afirka

By
Bakoji
-
January 29, 2025
Arewa Award

Hukumar kula da kwallon kafa ta Afirka (CAF) ta tabbatar da ranar da za a buga gasar cin kofin nahiyar Afirka (CHAN) na shekarar 2024 da aka ɗage a baya.

Hukumar kwallon kafar Afirka ta bayyana cewa a yanzu za a gudanar da gasar ta CHAN daga ranar 2 ga watan Agusta zuwa 30 ga watan Agustan 2025.

Tun a watan Fabrairun 2025 ne aka shirya gudanar da gasar karo na takwas, wanda kasashen Kenya, Tanzania da Uganda za su dauki nauyin shirya gasar, amma an dage gasar saboda kalubalen samar da ababen more rayuwa da ingantattun wurare.

An tabbatar da sabuwar ranar da za a gudanar da gasar ne a yayin taron kwamitin zartarwa na CAF da aka gudanar a ranar Litinin a birnin Rabat na kasar Morocco, karkashin jagorancin shugaban CAF Dr. Patrice Motsepe.

Read Also:

  • Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda
  • Gwamnan Jihar Katsina ya samar sabuwar ma’aikata a jihar
  • Za’a samar da sabbin jihohi 6 a Nijeriya

Gasar ta CHAN ta keɓenta ne ga ‘yan wasan da ke taka leda a gasannin cikin gida, kuma Senegal ce ke rike da kambun gasar, bayan da ta lashe gasar karshe da aka yi a Algeria.

Kwamitin zartarwa na CAF ya kuma yanke shawara kan wasu gasanni masu zuwa, da kuma fara gasar cin kofin Afrika ta mata ta da za a yi a Morocco daga 22-30 ga Afrilu 2025.

Wadanda su ka kai wasan karshe a gasar za su samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta mata ta (FIFA Futsal) da za a yi a Philippines a cikin shekara.

An kuma amince da wani sabon tsari na neman tikitin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afrika na U-17 na shekarar 2025, inda adadin kasashen da ke halartar gasar ya karu daga 12 zuwa 16.

Kwamitin zartaswa ya kuma amince da fara tsarin bayar da damar karbar bakuncin gasa a nan gaba, ciki har da gasar zakarun Turai ta mata (2005, 2026 & 2027), U-17 AFCON (2026, 2027 & 2028), da U-20 AFCON (2027, 2029 & 2031).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleECOWAS ta tabbatar da ficewar Nijar, Burkina Faso da kuma Mali a hukumance
Next articleGwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air
Bakoji

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INEC

NAHCON ta bayyana dalilian da suka saka Saudiya rage mata kujerun aikin hajji bana

Gwamnatin Najeriya ta cire darasin Lissafi cikin sharuɗan samun gurbin karatun Jami’a ga wasu ɗaliban

Za a karɓe wa ƴan Najeriyar da aka samu da laifi a waje fasfo na shekara 10

Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC

DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X

Sojojin Nijeriya sun hallaka mayakan boko haram 5 a jihohin Borno da Taraba

NDLEA ta kama Ba’indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a Legas

Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15

Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

Recent Posts

  • Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda
  • Gwamnan Jihar Katsina ya samar sabuwar ma’aikata a jihar
  • Za’a samar da sabbin jihohi 6 a Nijeriya
  • Jami’ar ABU ta musanta labarin samar da makamin Nukiliya
  • Mayakan Boko Haram sun fara kai hari da jirage marasa matuki a Borno

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1595 days 2 hours 58 minutes 56 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1577 days 4 hours 40 minutes 21 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam SandaGwamnan Jihar Katsina ya samar sabuwar ma'aikata a jiharZa'a samar da sabbin jihohi 6 a NijeriyaJami'ar ABU ta musanta labarin samar da makamin NukiliyaMayakan Boko Haram sun fara kai hari da jirage marasa matuki a BornoBabu wasu bayanan an yi wa masu bin wani addini kisan ƙare dangi - SultanZa ayi bincike kan masu laifin da Tinubu ya yiwa AfuwaTinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniyaMajalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INECNAHCON ta bayyana dalilian da suka saka Saudiya rage mata kujerun aikin hajji banaDalilin da ya sa Amnesty ke neman a soke hukuncin kisa a NajeriyaGwamnan jihar Bayelsa, ya fice daga jam'iyyarsa ta PDP.Tinubu ya buƙaci majalisar dattawa ta amince da naɗin Joash AmupitanGwamnatin Najeriya ta cire darasin Lissafi cikin sharuɗan samun gurbin karatun Jami'a ga wasu ɗalibanGwamnan Enugu ya koma APC bayan ficewa daga PDP
X whatsapp