• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General An saka ranar gudanar da gasar CHAN ta Afirka
  • General
  • WASANNI

An saka ranar gudanar da gasar CHAN ta Afirka

By
Bakoji
-
January 29, 2025
Arewa Award

Hukumar kula da kwallon kafa ta Afirka (CAF) ta tabbatar da ranar da za a buga gasar cin kofin nahiyar Afirka (CHAN) na shekarar 2024 da aka ɗage a baya.

Hukumar kwallon kafar Afirka ta bayyana cewa a yanzu za a gudanar da gasar ta CHAN daga ranar 2 ga watan Agusta zuwa 30 ga watan Agustan 2025.

Tun a watan Fabrairun 2025 ne aka shirya gudanar da gasar karo na takwas, wanda kasashen Kenya, Tanzania da Uganda za su dauki nauyin shirya gasar, amma an dage gasar saboda kalubalen samar da ababen more rayuwa da ingantattun wurare.

An tabbatar da sabuwar ranar da za a gudanar da gasar ne a yayin taron kwamitin zartarwa na CAF da aka gudanar a ranar Litinin a birnin Rabat na kasar Morocco, karkashin jagorancin shugaban CAF Dr. Patrice Motsepe.

Read Also:

  • Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurka
  • rahotannin daga jihar Katsina na cewa ‘Yan bindiga sun kashe mutum 9 a jihar
  • ‘Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026’

Gasar ta CHAN ta keɓenta ne ga ‘yan wasan da ke taka leda a gasannin cikin gida, kuma Senegal ce ke rike da kambun gasar, bayan da ta lashe gasar karshe da aka yi a Algeria.

Kwamitin zartarwa na CAF ya kuma yanke shawara kan wasu gasanni masu zuwa, da kuma fara gasar cin kofin Afrika ta mata ta da za a yi a Morocco daga 22-30 ga Afrilu 2025.

Wadanda su ka kai wasan karshe a gasar za su samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta mata ta (FIFA Futsal) da za a yi a Philippines a cikin shekara.

An kuma amince da wani sabon tsari na neman tikitin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afrika na U-17 na shekarar 2025, inda adadin kasashen da ke halartar gasar ya karu daga 12 zuwa 16.

Kwamitin zartaswa ya kuma amince da fara tsarin bayar da damar karbar bakuncin gasa a nan gaba, ciki har da gasar zakarun Turai ta mata (2005, 2026 & 2027), U-17 AFCON (2026, 2027 & 2028), da U-20 AFCON (2027, 2029 & 2031).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleECOWAS ta tabbatar da ficewar Nijar, Burkina Faso da kuma Mali a hukumance
Next articleGwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air
Bakoji

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

‘Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026’

Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano – NHRC

Shugaban Najeriya zai iya dakatar da gwamna – Kotun Ƙoli

NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Kwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin Nijeriya

NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

KAROTA ta bukaci Al’ummar jihar Kano su bawa jami’anta hadin kai

Gwamnatin Neja ta ɗora alhakin sace ɗalibai kan makarantar

Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai

SAEMA 2025: IMPR Ta kaddamar da Littafi Kan Yaki da Sha da fatauci miyagun ƙwayoyi da fasa kwauri

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara karɓar harajin man fetur

Recent Posts

  • Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurka
  • rahotannin daga jihar Katsina na cewa ‘Yan bindiga sun kashe mutum 9 a jihar
  • ‘Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026’
  • Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe 74 ke fara aiki
  • Mayakan Boko Haram sun kutsa cikin ayarin sojin Najariya da bama-bamai a Borno

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1681 days 48 minutes 9 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1663 days 2 hours 29 minutes 34 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurkarahotannin daga jihar Katsina na cewa 'Yan bindiga sun kashe mutum 9 a jihar'Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026'Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe 74 ke fara aikiMayakan Boko Haram sun kutsa cikin ayarin sojin Najariya da bama-bamai a BornoSojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin TimbuktuAbba da Tinubu sun tattauna kan tsaro da ci gaban Kano - Dawakin TofaƳanbindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 160 a coci a KadunaMun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano - NHRCƳansanda a jihar Nasarawa sun tseratar da yara 17 da ake shirin safararsuSojoji sun lalata sansanonin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin NajeriyaTinubu ya yi tir da kisan mace da ƴaƴanta shida a KanoKisan gilla - Ƴansandan jihar Kano sun kama wadanda ake zargi da ƴaƴantaƳan sanda sun fara bincike kan mutum 6 da aka yiwa yankan rago a JiharGwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji
X whatsapp