• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General An saka ranar gudanar da gasar CHAN ta Afirka
  • General
  • WASANNI

An saka ranar gudanar da gasar CHAN ta Afirka

By
Bakoji
-
January 29, 2025
Arewa Award

Hukumar kula da kwallon kafa ta Afirka (CAF) ta tabbatar da ranar da za a buga gasar cin kofin nahiyar Afirka (CHAN) na shekarar 2024 da aka ɗage a baya.

Hukumar kwallon kafar Afirka ta bayyana cewa a yanzu za a gudanar da gasar ta CHAN daga ranar 2 ga watan Agusta zuwa 30 ga watan Agustan 2025.

Tun a watan Fabrairun 2025 ne aka shirya gudanar da gasar karo na takwas, wanda kasashen Kenya, Tanzania da Uganda za su dauki nauyin shirya gasar, amma an dage gasar saboda kalubalen samar da ababen more rayuwa da ingantattun wurare.

An tabbatar da sabuwar ranar da za a gudanar da gasar ne a yayin taron kwamitin zartarwa na CAF da aka gudanar a ranar Litinin a birnin Rabat na kasar Morocco, karkashin jagorancin shugaban CAF Dr. Patrice Motsepe.

Read Also:

  • Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC
  • DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X
  • Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-

Gasar ta CHAN ta keɓenta ne ga ‘yan wasan da ke taka leda a gasannin cikin gida, kuma Senegal ce ke rike da kambun gasar, bayan da ta lashe gasar karshe da aka yi a Algeria.

Kwamitin zartarwa na CAF ya kuma yanke shawara kan wasu gasanni masu zuwa, da kuma fara gasar cin kofin Afrika ta mata ta da za a yi a Morocco daga 22-30 ga Afrilu 2025.

Wadanda su ka kai wasan karshe a gasar za su samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta mata ta (FIFA Futsal) da za a yi a Philippines a cikin shekara.

An kuma amince da wani sabon tsari na neman tikitin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afrika na U-17 na shekarar 2025, inda adadin kasashen da ke halartar gasar ya karu daga 12 zuwa 16.

Kwamitin zartaswa ya kuma amince da fara tsarin bayar da damar karbar bakuncin gasa a nan gaba, ciki har da gasar zakarun Turai ta mata (2005, 2026 & 2027), U-17 AFCON (2026, 2027 & 2028), da U-20 AFCON (2027, 2029 & 2031).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleECOWAS ta tabbatar da ficewar Nijar, Burkina Faso da kuma Mali a hukumance
Next articleGwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air
Bakoji

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC

DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X

Sojojin Nijeriya sun hallaka mayakan boko haram 5 a jihohin Borno da Taraba

NDLEA ta kama Ba’indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a Legas

Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15

Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

‘Yan sandan Jigawa sun kama Dilolin kwaya a jihar

Kofa ya sanar da ficewarsa da ga NNPP

Gwamnatin Najeriya ta yi maraba da ɗaure Simon Ekpa a Finland

Atiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Rivers

Recent Posts

  • Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC
  • DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X
  • Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-
  • Gwamnan Kano ya tarɓi masu zanga-zangar ƙin kalaman Lawan Triumph
  • Gwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1571 days 23 hours 28 minutes 26 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1554 days 1 hour 9 minutes 51 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu - INECDSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin 'aibata' Tinubu a shafin XGwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-Gwamnan Kano ya tarɓi masu zanga-zangar ƙin kalaman Lawan TriumphGwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jiniƳan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan KatsinaRundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami'anta a Jihar BenueNasarar da Daliban Kano suka Samu a NECO kokarin Ganduje ne - Sanusi KiruWata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami'an KAROTA umarniSojojin Najeriya sun cafke kwamandan IPOBƳanbindiga sun hallaka mutum 22 a Jamhuriyyar NijarSojojin Nijeriya sun hallaka mayakan boko haram 5 a jihohin Borno da TarabaNDLEA ta kama Ba'indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a LegasLikitoci a Najeriya sun janye yajin aikin gargaɗiKotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15
X whatsapp