Home General Gwamnan Kano ya bawa Jami’ar Bayero Umarnin dakatar da rushe-rushe a Rimin...

Gwamnan Kano ya bawa Jami’ar Bayero Umarnin dakatar da rushe-rushe a Rimin zakara

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bawa Jami’ar Bayero umarnin dakatar da rushe -rushen da ta ke yi a garin Rimin Zakara.

Gwamnan ya bada umarnin ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziya da kuma jajen abinda ya faru ga alummar yankin.

Abba Kabir ya kuma yiwa alummar alkawarin kawo karshen rikicin filayen da ke gudana tsakanin Jami’ar BUK da alummar Rimin Zakara wanda ya shafe sama da shekaru 30.

Dangane da wadanda suka rasa rayukansu gwamna Abba kabir ya bayar da umarnin kafa wani kwamiti da zai binciki lamarin tare da daukar dawainiyar iyalansu.

Hakazalika Gwamnan ya ba da umarni samawa alummar yankin asibitin sha -ka-tafi tare da Gina musu masallacin juma’a.

Gwamnan Abba Kabir Yusuf na bayar da umarnin daukar nauyin wadanda Suka Sami raunuka sakamakon abinda ya faru a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp