Wasu gwamnoni 11 karkashin jam’iyyar PDP, sun shigar da ƙara gaban kotun koli inda suke kalubalantar dakatarwar da shugaba Bola Tinubu ya yi wa zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara.
Ƙarar da gwamnonin suka shigar ranar Talata, na kuma kalubalantar ayyana dokar ta-baci da aka yi a jihar.
Gwamnonin jihohi da suka shigar da ƙarar sun haɗa da Adamawa da Enugu da Osun da Oyo da Bauchi da Akwa Ibom da Plateau da Delta da Taraba da Zamfara da kuma Bayelsa.
A ƙarar da suka shigar, gwamnonin na kuma son kotun kolin ta ayyana cewa ko shugaban ƙasa na da ikon dakatar da zaɓaɓɓen gwamna na jiha.
Sun kuma buƙaci kotun ta yanke hukuncin cewa ko yadda shugaban ƙasa ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar ta Ribas bai saɓa wa kundin tsarin mulki na 1999 ba.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 14 hours 47 minutes 17 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 28 minutes 42 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com