Home AFIRKA Mayaƙan JNIM da ‘yan tawayen FLA sun ƙaddamar da hari kan tawagar...

Mayaƙan JNIM da ‘yan tawayen FLA sun ƙaddamar da hari kan tawagar sojin Mali

Rundunar sojin Mali ta bayyana cewa, wasu da ake zargi masu iƙirarin jihadi ne tare da haɗin gwiwar ‘yan tawayen FLA, sun ƙaddamar da wani mummunan hari akan wata tawagar sojojin ƙasar a ranar Litinin ɗinnan da ta gabata, a yankin arewacin ƙasar. Sai dai rundunar bata ba da cikakken bayani kan yadda lamarin ya kasance ba.

Bayanai sun nuna cewa bayan da maharan suka kammala aika-aikar tasu a Kidal da safiyar ranar Litinin ɗin, sai suka zarce yankin Anefis domin aiwatar da wata manufar tasu.

Sannan yan tawayen FLA suka bayyana cewa wannan harin sun iske motoci guda hudu a wurin, ciki har da mota mai sulke guda daya, a yayin da suka yi ikirarin cewa sun kwashesu tare da ikirarin cewa sun yi sanadin sanadin mutuwar mutane da dama.

Rundunar sojin Mali a cikin wata sanarwa da ta fitar a wannan Litinin, ta ce an yi arangama, amma ba tare da ba da cikakken bayani kan taho mu gamar da suka yi ba.

Sai dai ‘yan tawayen na FLA sun ba da wata sanarwa akan harin da jirgi mara matuƙi ya kai musu a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp