Home SIYASA Abubuwan da Zan Cimma Idan na Zama Shugaban Kasa a 2023 –...

Abubuwan da Zan Cimma Idan na Zama Shugaban Kasa a 2023 – Gwamna Wike

Abubuwan da Zan Cimma Idan na Zama Shugaban Kasa a 2023 – Gwamna Wike

 

Gwamnan jihar Ribas, ya bayyana abubuwan da yake so ya cimma idan ya zama shugaban kasa a zaben 2023.

Ya bayyana cewa, yana da yakinin dawo da zaman lafiya kasar nan matukar aka zabe shi domin ya gaje Buhari.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa, Najeriya na bukatar shugaba kamarsa domin ciyar da kasar gaba da magance matsaloli.

Benue- Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas ya ce da yardar Allah zai lashe zaben shugaban kasa na 2023 da aka sa a gaba.

Wike ya bayyana hakan ne a yayin wani taron tuntuba da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP reshen Benue a gidan gwamnati da ke Makurdi a ranar Lahadi.

Hakan na zuwa ne kwana guda bayan da gwamnan na jam’iyyar PDP ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a karon farko a zabe mai zuwa, kamar yadda ya tada a Twitter.

Wike ya ci gaba da cewa, tare da jama’a za su aiwatar da wani tsari na hadin gwiwa don dawo da zaman lafiya da tsaro a ‘yan Najeriya.

Ya kuma sha alwashin magance matsalar rashin tsaro kwata-kwata a kasar matukar ya zama shugaba a 2023.

Ba Wike kadai bane dan jam’iyyar PDP da ya bayyana aniyar tsayawa takara a zaben mai zuwa ba.

Da yake amsa tambaya kan abin da zai yi na daban ga kasar nan idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa, Gwamna Wike ya sha alwashin magance matsalar rashin tsaro da ke kara kamari a kasar.

Gwamnan wanda ya yi Allah wadai da harin ta’addancin da aka kai a filin jirgin sama na Kaduna a karshen mako, ya ce ‘yan Najeriya na bukatar shugaba mai daukar matakin gaggawa da zai magance matsalar rashin tsaro a kasar.

Da yake nasa jawabin, Wike ya bayar da tabbacin cewa idan aka zabe shi, gwamnatinsa za ta samar da doka da oda domin a samu karin hannayen jarin kasashen waje kai tsaye zuwa kasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp