Home SIYASA Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ayyana Dokar Hana Amfani da ‘Yan Daba a...

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ayyana Dokar Hana Amfani da ‘Yan Daba a Zaben 2023

Gwamnan jihar Katsina ya ayyana dokar hana amfani da ‘yan daba a zaben 2023 mai zuwa nan da badi.

Ya bayyana hakan ne ta bakin mai ba shi shawari kan harkokin tsaro, ya kuma ba ‘yan siyasa shawari mai kyau.

Gamayyar kungiyar farar hula ta yabawa gwamnan, ta kuma bayyana kwarin gwiwar samun zabe na gari a Katsina.

Jihar Katsina – A kokarin tabbatar da zaben 2023 cikin aminci, gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya sanya hannun kan dokar hana damawa da ‘yan daba a gangamin zabe a fadin jiharsa, AIT ta ruwaito.

Gwamnan ya bayyana wannan ne ta bakin mai ba shi shawari kan harkokin tsaro, Ibrahim Katsina, kuma ya ce hakan zai taimaka wajen tabbatar da zaban shugabannin da suka dace a zaben da za yi.

Ya kuma bayyana cewa, tunda wannan ne zaben karshe da za a yi a mulkin Masari, yana da kyau a yi shi cikin aminci domin kafa tarihi na gari a jihar.

Hakazalika, ya ce gwamna Masari dattijon kasa ne, kuma zai tabbatar da zaman lafiya a jihar, musamman a kokarinsa na dawo da martabar jihar a matsayin kasa mai tarbar baki.

Ku dauki ‘ya’yan talakawa kamar naku, Masari ga ‘yan siyasa

Daga karshe ya shawarci ‘yan siyasa da suke yiwa ‘yan daba kallon ‘ya’yansu kuma ya kamata su ba su wadataccen ilimi a madadin bata rayuwarsu ta hanyar mai dasu tsageru.

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Farar Hula ta CCSO, Abdulrahman Abdullahi ya yaba da kokarin Masari na damawa da ‘yan daba, tare da bayyana cewa hakan zai tabbatar da zabe na gari a Katsina.

Daga nan ne ya ce, idan gwamnati ta tabbatar da cikakken amfani da dokar, zai zama mafi alherin abin da gwamnan ya assasa.

Ko da a baya an taba jiyo yadda gwamnan ya yi irin wannan hani a watan Fabrairun 2022.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp