Home DUNIYA Rikicin Kibilanci na ci gaba da Tsananta a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Rikicin Kibilanci na ci gaba da Tsananta a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

Ana cigaba da bincike kan rikicin daya haddasa mutuwar akalla mutane 20 cikin makon nan a rikicin kabilancin da ke ci gaba da tsananta tsakanin kabilar Yaka da Teke na lardin Mai-Ndombe a Mahukuntan Jamhuriyar Demokradiyar Congo.

Tsawon watanni ana fama da rikicin kabilancin a yankin Mai-Ndombe inda alkaluman gwamnatin kasar ke cewa daga faro fadan a watan Yunin da ya gabata zuwa yanzu an kashe fararen hulan da yawansu yah aura 180 ciki har da wasu 16 a makon jiya kari kan mutane 20 da aka kashe a cikin makon nan.

Majiyoyi daga yankin sun ce rikicin ya faro bayan takaddama game da biyan haraji lamarin da zuwa yanzu ya tilasta dubunnan mutane daga kabilun biyu na Yaka da Teke tserewa daga yankunansu don tsira da rayukansu.

Duk da cewa kamfanin dillancin labaran Faransa ya gaza tattara hakikanin alkaluman mutanen da rikicin ya daidaita da kuma wadanda suka mutu, amma Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa matukar ba a dauka matakan da suka kamata ba, rikicin ka iya juyewa zuwa mafi muni.

Rahotanni sun ce a litinin din da ta gabata ne, wasu maharan kabilar Yaka rike manyan bindigu suka farwa kauyen Teke lamarin da ya sanya al’ummar garin kare kansu ta hanyar daukar makamai inda nan take akayi asarar rayukan mutane akalla 20.

Wani ganau a yankin na Teke, Nkete Mboma Butu y ace adadin mutanen da suka mutu ka iya zarta alkaluman da mahukuntan kasar suka bayyana la’akari da yadda aka samu asarar rayuka daga dukkanin bangarorin biyu.

Da ya ke bayar da bahasi kan rikicin na makon nan yayin jawabinsa gaban wakilan gwamnati a Kinshasa mataimakin shugaban yankin Moise Makami Muzik ya ce alkaluman mutanen da suka mutu a rikicin ya haura 35.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp