Home General Buhari ya yabawa Ganduje bisa asibitin Masu fama da cutar daji a...

Buhari ya yabawa Ganduje bisa asibitin Masu fama da cutar daji a jihar Kano

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yabawa gwamnan jihar kano Abdullahi Umar Ganduje bisa Samar da asibitin Masu fama da cutar daji a jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya.
Buhari ya bayyana haka  ne lokacin da yake bude asibitin dake unguwar giginyu a karamar hukumar Nasarawa ta jihar kano.
Buhari yace dole a ya yabawa hangen nesa na gwamna Ganduje na samar da Asibitin Saboda yadda zai taimaka wajen magance fita waje domin neman lafiya da Kuma bunkasa tattalin arzikin Nigeria.
A nasa jawabin gwamnan jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce an samar da Asibitin ne don rage yawan fita kasashen waje domin neman lafiya.
Yace asibitin shi ne irinsa na farko a Nigeria da Africa baki daya, Kuma zai bunkasa tattalin arzikin jihar kano da kasa baki daya.
An dai sanyawa Asibitin sunan Mai dakin gwamnan kano Farfesa Hafsat Abdullahi Ganduje.
Bayan nan Shugaba Buhari ya bude katafariyar Gadar dake Hotoro wacce aka Saka mata sunan Muhammadu Buhari, da gidajen gwamnatin tarayya dake Darmanawa da Kuma Cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote dake kan titin Zaria da dai sauran su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp