Home General Buhari ya yabawa Ganduje bisa asibitin Masu fama da cutar daji a...

Buhari ya yabawa Ganduje bisa asibitin Masu fama da cutar daji a jihar Kano

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yabawa gwamnan jihar kano Abdullahi Umar Ganduje bisa Samar da asibitin Masu fama da cutar daji a jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya.
Buhari ya bayyana haka  ne lokacin da yake bude asibitin dake unguwar giginyu a karamar hukumar Nasarawa ta jihar kano.
Buhari yace dole a ya yabawa hangen nesa na gwamna Ganduje na samar da Asibitin Saboda yadda zai taimaka wajen magance fita waje domin neman lafiya da Kuma bunkasa tattalin arzikin Nigeria.
A nasa jawabin gwamnan jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce an samar da Asibitin ne don rage yawan fita kasashen waje domin neman lafiya.
Yace asibitin shi ne irinsa na farko a Nigeria da Africa baki daya, Kuma zai bunkasa tattalin arzikin jihar kano da kasa baki daya.
An dai sanyawa Asibitin sunan Mai dakin gwamnan kano Farfesa Hafsat Abdullahi Ganduje.
Bayan nan Shugaba Buhari ya bude katafariyar Gadar dake Hotoro wacce aka Saka mata sunan Muhammadu Buhari, da gidajen gwamnatin tarayya dake Darmanawa da Kuma Cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote dake kan titin Zaria da dai sauran su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a Kano
X whatsapp