Home General Rundunar “yan Sanda sun haramta hawan Sallah a Jihar Kano

Rundunar “yan Sanda sun haramta hawan Sallah a Jihar Kano

Rundunar ‘yan sanda ta kasa reshen jihar kano ta ce ta haramta hawan salla yayin bukukuwan Babbar Sallah a jihar Kano.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanyawa hannu kuma aka raba ga manema labarai a jihar.

Sanarwar ta ce rundunar ta dauki wannan matakin ne sakamakon barazanar tsaro da za a iya samu idan an gudanar da hawan sallar.

”Bayan ganawa da duk masu ruwa da tsaki a jihar kano, Rundunar yan sandan jihar kano ta hana yin duk wani hawa a yayin bikin sallah babbar dake tafe” a cewar Sanarwar.

Rundunar ta ce ta haramta hawan a dukkanin fadin jihar kano baki daya.

Rundunar ta bukaci al’ummar jihar da su gudanar da sallar idin su cikin kwanciyar hankali da lumana a inda suke, su kuma cigaba da baiwa rundunar hadin kai don cigaba da inganta tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp