Home General Tinubu yace zai magance rikicin Manoman da Makiyaya

Tinubu yace zai magance rikicin Manoman da Makiyaya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na baƙin ƙoƙarinta wajen lalubo hanyoyin magance rikice-rikicen manoma da makiyaya.

Yayin da yake jawabi bayan sanya hannu da wasu kamfanin sarrafa nama na JBS a birnin Rio de Janeiro na ƙasar Brazil, Shugaba Tinubu ya ce rikicin manoma da makiyaya ya jima yana haifar da asarar dukiyoyi a wasu yankunan Afirka.

”Rikici tsakanin manoma da makiyaya da ke haifar da asarar rayuka da zubar da jini, idan aka yi amfani da dabarun zamani da wayewa wajen magancenta, zai kawo ci gaban tattalin arzikinmu”, in ji shugaban ƙasar.

Bayan ƙulla yarjejeniyar kamfanin sarrafa nama na JBS ya amince da zuba jarin dala miliyan 2.5 domin gina kamfanonin sarrafa nama shida a faɗin Najeriya.

Kamfanin ya ce uku daga cikin kamfanonin za su mayar da hankali wajen sarar naman kaji, ayayin da biyu za su sarrafa jan nama, sai kuma guda wanda zai sarrafa nama aladu.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta mayar da hankali wajen gayyato masu zuba jari daga ciki da wajen ƙasar a ɓangaren kiwon dabbobi da noma, lamarin da ya ce zai taimaka wajen magance rikici tsakanin manoman da makiyaya, tare da yaƙar yunwa da talauci da inganta ci gaban tattalin arziki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp