Home General Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara...

Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano – NHRC

Hukumar kare haƙƙin ɗan adam ta Najeriya NHRC ta sanar da karɓar ƙorafe-ƙorafen take haƙƙin ɗan adama har dubu 3 da 19 tsakanin watan Janairu zuwa Disamban shekarar da ta gabata a jihar Kano kaɗai.

Cikin ƙorafe-ƙorafen da ke gaban hukumar masu alaƙa da cin zarafin mata da ƙananan yara su ne kan gaba a jihar ta Kano, kamar yadda alƙaluman hukumar ke nunawa.

Shugaban hukumar a jihar ta Kano Shehu Abdullahi da ke sanar da hakan ga manema labarai a yau Litinin ya ce cikin ƙorafe-ƙorafen fiye da dubu 3 da aka gabatar gabansu sun yi nasarar magance dubu 2 da 276.

Shugaban hukumar ta NHRC a Kano, ya kuma ce yanzu haka hukumar na aiki kan ƙorafe-ƙorafe 743 da basu kai ga kammala warwarewa ba.

A cewar shugaban na NHRC galibin ƙorafe-ƙorafen da aka fiya miƙa musu a jihar ta Kano sun fi shafar batutuwa masu alaƙa da watsi da baiwa yara kulawa, ko kuma take haƙƙin yaran, kana cin zarafi a cikin gidajen aure sai take haƙƙin zamantakewa ko na rayuwa sai kuma batutuwa masu alaƙa da al’adu da zamantakewar iyali.

Shugaban na NHRC ya ce sauran ƙorafe-ƙorafen da hukumar ke samu sun shafi cin zarafi daga jami’an tsaro, cin zarafi ta hanyar lalata musamman ga mata kana matsalar iyaye ta rashin ɗaukar nauyin iyalansu da sauran ƙorafe-ƙorafe masu alaka da rayuwar yau da kullum.

Shugaban hukumar kare haƙƙin bil’adaman ta Najeriya rashen jihar Kano Abdullahi Shehu ya sha alwashin ɗaukar gaɓarar fara aikin wayar da kan jama’a hatta a yankunan karkara ciki har da shirya taruka na musamman don ankarar da jama’a kan haƙƙoƙinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp