Home General Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara...

Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano – NHRC

Hukumar kare haƙƙin ɗan adam ta Najeriya NHRC ta sanar da karɓar ƙorafe-ƙorafen take haƙƙin ɗan adama har dubu 3 da 19 tsakanin watan Janairu zuwa Disamban shekarar da ta gabata a jihar Kano kaɗai.

Cikin ƙorafe-ƙorafen da ke gaban hukumar masu alaƙa da cin zarafin mata da ƙananan yara su ne kan gaba a jihar ta Kano, kamar yadda alƙaluman hukumar ke nunawa.

Shugaban hukumar a jihar ta Kano Shehu Abdullahi da ke sanar da hakan ga manema labarai a yau Litinin ya ce cikin ƙorafe-ƙorafen fiye da dubu 3 da aka gabatar gabansu sun yi nasarar magance dubu 2 da 276.

Shugaban hukumar ta NHRC a Kano, ya kuma ce yanzu haka hukumar na aiki kan ƙorafe-ƙorafe 743 da basu kai ga kammala warwarewa ba.

A cewar shugaban na NHRC galibin ƙorafe-ƙorafen da aka fiya miƙa musu a jihar ta Kano sun fi shafar batutuwa masu alaƙa da watsi da baiwa yara kulawa, ko kuma take haƙƙin yaran, kana cin zarafi a cikin gidajen aure sai take haƙƙin zamantakewa ko na rayuwa sai kuma batutuwa masu alaƙa da al’adu da zamantakewar iyali.

Shugaban na NHRC ya ce sauran ƙorafe-ƙorafen da hukumar ke samu sun shafi cin zarafi daga jami’an tsaro, cin zarafi ta hanyar lalata musamman ga mata kana matsalar iyaye ta rashin ɗaukar nauyin iyalansu da sauran ƙorafe-ƙorafe masu alaka da rayuwar yau da kullum.

Shugaban hukumar kare haƙƙin bil’adaman ta Najeriya rashen jihar Kano Abdullahi Shehu ya sha alwashin ɗaukar gaɓarar fara aikin wayar da kan jama’a hatta a yankunan karkara ciki har da shirya taruka na musamman don ankarar da jama’a kan haƙƙoƙinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp