Home SIYASA Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), a yau ya halarci taron karrama mai girma gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, (MON, MNI), wanda ƙungiyar cigaban ƙasar Haɗejia, (Haɗejia Ina Mafita Initiative) ta yi.

Taron ya samu halartar mai girma mataimakin gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi Ɗan Moɗi, da mai girma kakakin majalissar dokoki na Jihar Jigawa, Onarabul Idris Garba Kareka, da mai martaba sarkin Haɗejia, kana kuma shugaban majalissar sarakunan Jihar Jigawa, Dakta Adamu Abubakar Maje Haruna, (CON), da mai girma sanatan ƙasar Haɗejia, Barista Ibrahim Hassan Haɗejia, (Shatiman Haɗejia Na Biyu), da mai girma tsohon shugaban hukumar kula da shige da fice ta ƙasa, (NIS), Alhaji Muhammad Babandede,

Sai kuma ƴan majalissar wakilai na tarayya da ƴan majalissar dokokin Jiha, da shugabannin ƙananan hukumomi da sauran muhimman mutane da dama na ƙasar Haɗejia da Jigawa.

Daga bisani kuma kafin ya komawa birnin tarayya, Abuja, mai girma shugaba ya karɓi baƙuncin al’umma daban-daban, dattawa, matasa, da kuma ƴan ƙungiyoyi, waɗanda su ka haɗa da: ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyi magoya bayan shugaban ƙasa Malam Muhammadu Buhari, (GCFR), “Coalition Of Buhari Support Groups”, (COBSG), ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar, Onarabul Musa Gambo Guri, waɗanda su ka kai masa ziyarar girmamawa tare da godiya a bisa wakilci da ya aike wurin babban taron ƙungiyar na shiyar Arewa Maso Yamma da aka yi a Jihar Jigawa.

Kana kuma, ya karɓi baƙuncin wasu daga cikin matasan da su ka samu horo kan ilimin gyaran wayar salula da sauran harkokin fasaha na zamani wanda hukumarsa ta gudanar a kwanan nan, inda su ka ziyarce shi domin yi masa godiya da yabawa kan ƙoƙarin da ya ke wajen ɗora rayuwar matasa kan harkar cigaba domin bunƙasa cigaban ƙasa da duk al’umma.

Lahadi, 6 ga watan Janairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp