Home SIYASA Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon firaministan Mali Soumeylou Boubèye Maïga – wanda ke fuskantar shari’a saboda tuhumar da ake masa ta cin hanci da rashawa – ya mutu yana mai shekara 67 da haihuwa.

Mista Maiga ya mutu ne ranar Litinin a wani asibiti a Bamako, babban birnin kasar, kamar yadda iyalansa suka sanar.

Iyalan nasa sun ce an kama shi kuma an tsare da shi karkashin wani hali mai tayar da hankali. A watan Disamba aka kwantar da shi a asibiti.

Kamfanin dillancin labarai na Associated Press ya ce gwamnatin ƙasar ta ki amincewa da bukatarsa ta zuwa kasashen waje domin a duba lafiyarsa.

Sai dai ta mika sakonta na ta’aziyya ga iyalan tsohon firaministan, bayan ta fitar da wata sanarwa da ke cewa ya mutu ne bayan wata doguwar jinya da ya yi.

An dai kama Mista Maiga ne a watan Agustan bara kuma aka tsare shi bayan da aka tuhume shi da aikata laifukan cin hanci da rashawa kan yadda aka sayo wani jirgin sama na shugaban kasa, yayin mulkin hambararren shugaban kasar Ibrahim Boubacar Keïta.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp