Home General CBN yace bankuna zasu cigaba da karbar tsuffin kudi bayan wa’adi ya...

CBN yace bankuna zasu cigaba da karbar tsuffin kudi bayan wa’adi ya kare

Gwamnan Babban Bankin Najeriya Godwin Emefiele ya ce bankunan ƙasar za su ci gaba da karɓar tsoffin takardun kuɗi daga hannun kwastomominsu har zuwa bayan wa’adin 10 ga watan Fabrairu, lokacin da za a daina amfani da tsoffin takardun kuɗin a ƙasar

Mista Emefiele ya bayyana hakan ne a lokacin da ya hallara a gaban kwamitin wucin-gadi kan sauya fasalin kuɗin ƙasar na majalisar wakilan ƙasar.

To sai dai gwamnan Babban Bankin bai bayyana lokacin da bankunan za su daina karɓar tsoffin takardun kuɗin ba.

Tun da farko dai kakakin Majalisar Wakilan ƙasar Femi Gbajabiamila, ya zargi gwamnan Babban Bankin da saɓa wa sashe na 20 na dokar CBN wadda a cewarsa ta wajabta wa bankunan ci gaba da karɓar tsoffin kudin har zuwa bayan wa’adin da Babban Bankin ya saka.

Yayin da yake jawabi a gaban kwamitin Emefiele, ya ce ya yarda da ‘yan majalisar game da sashe na 20 na dokar CBN.

”Sashe na 20 na cewa bayan cikar wa’adi za a daina amfani da tsoffin takardun kuɗi, to amma an wajabta wa bankuna karɓar ƙuɗaɗen. Dan haka ina tare da majalisa a kan haka”, in ji Emefiele.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp